Page 5

258 19 0
                                    


Koda suka komo ciki bata yi masa magana ba illa zama a kan kujera data yi ta shiga latsa waya.

Zama yayi kusa da ita yace "Azizaty mey nayi?" Ya tambaya.

Shiru tayi bata ce komai ba.

"Please say something ko naji sanyi my Azizaty".

Yanda yayi maganar yasa ta kusa dariya amma seta maze ta cigaba da kallon waya.

" Ayya azizaty inde dan ban dawo da wuri bane ina me neman afuwa ,dubiya muka je da abokaina wayata kuma ba charge shiyasa ban kira ki ba". Ahmad ya fad'a.

"Toh amma kasan zan damu dayawa aikoh da seka kirani da wata wayar". Cewar Reyhana cikin shagwaba.

" Sorry my Azizaty next time haka bazata faru ba kinji".

Kai kawai ta kad'a bata ce komai ba.

"Kin ha'kura?" Ya tambaya tare da tallafo ha'barta.

"Smile my one and only always and forever". Ya fad'a.

Hakan yasa ta saki murmushi ,shi kuwa hugging d'inta yayi tightly " I love you Azizaty.Ya furta

"I love you too dear". Ta fad'a itama ta sake 'kan'kameshi.

***

Ta 'bangaren Mommy kuwa Walida bayan sun koma take nuna wa Ikram alewar da Reyhana ta bata.Mommy ta'ba baki tayi dan tana zaune a palour.

" Wai sunan gidan Amarya aka je shine aka 'kare da wannan mtchhwww!" Mommy ta fad'a tare da tsaki.

Ita Walida bata ji me Mommy tace ba amma Ikram taji tayi gum da bakinta.

Washegari...

Kasancewar weekend Ahmad yana gida throughout be fita ba ,suna sitting room abunsu suna kallo a TV Reyhana ta d'ora kanta a cinyarsa.

Wayar Reyhana ce tayi ringing hakan yasa ta tashi,koda ta duba taga Mommy bayan sun gaisa Mommy take fad'a mata bikin wata cousin tasu Reyhana da za'ai.

"Mommy kisa Ikram ta kawo min invitation dan Allah". Reyhana ta fad'a.

" Idan ba'a kawo ba kenan bazaki jeba?" Mommy ta tambaya.

"A'a ba haka nake nufi ba wai da sena bawa ya Ahmad na d'aurin aure".Reyhana ta fad'a a sanyaye

" Bikin danginki ake ko nashi? dole seya je?" Mommy ta tambaya cikin fad'a.

Allah yasa lokacin Ahmad ya fita daga d'akin da ze iya ji.

"Eyyi baki amsan ba". Cewar Mommy.

"A'a ,toh Mommy Allah ya kaimu"Reyhana ta fad'a kwalla na cika a idanunta.

Daga haka sukai sallama gefe ta ajje wayar takaici ya isheta.Furucin Mommy ya bugi zuciyarta sosai taji ba dad'i koyaushe bata da buri irin Mommy ta dena tsanar mijinta ita da danginta."ko su Mommy basu kawo IV ba ai gidansu Amaryar sa kawo".Abinda ta fad'a a ranta kenan.

Tana cikin wannan batunne sega Ahmad ya shigo da sauri tayi 'ko'karin saita kanta karya gano wani abun.

" Da Mommy kikai waya?" Ya tambaya.

"Eh tana gaisheka".Reyhana ta fad'a.

Toh ina amsawa". Ya fad'a.

" Dama maganar biki ce ranar alhamis za'a fara". Reyhana ta fad'a.

"Ok toh Allah ya kaimu". Ahmad ya fad'a ba tare da ya sake cewa komai ba.

" Ranar friday d'aurin aure kuma". Ta fad'a.

Nan ma Allah ya kaimu yace.Reyhana a zuciyarta haushi ya mamaye dabadan ba da ba abinda zesa ta fad'a masa zancen d'aurin auren dande karya fuskanci ko da wani abun.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now