Page 26

182 21 0
                                    

    Tana ganin shigowar Umma tayi sauri ta mi'ke daga kwance,cikin rissinawa ta gaisheta.

     Umma fuskarta a sake ta amsa tare da fad'in."Yau ba makaranta kenan".

      "Eh".Ta amsa.

       " Dama naji ki shiru nace bari na duba ki".Umma ta fad'a.

       "Uhm yanzu dama nake son fitowa".Zainab ta fad'a fad'a tana sosa kai.

        Umma bata dad'e da fita daga d'akin ba Zainab ta fita itama,kamar koyaushe ta shiga kitchen taya ta had'a breakfast sede ta raba hankalinta biyu tana tunanin fitowar Ahmad.

•••

Mommy a tsugune ta tarar da Reyhana a kitchen d'in se sharar hawaye take,Nasreen tana daga gefe tana kallon Ummienta na kuka fuskarta itama kamar mey shirin yin kukan.

      " Reyhana meye haka? Menene?"Mommy ta tambaya.

      Shiru tayi bata ce komai ba sede yanzun tayi dena kuka,tashi tayi tsaye a daddafe tana share hawayen .

      "Kukan na meye? Mutum da giramansa yasa kuka ga yarinya babarta na kuka kince itama tayi kenan". Mommy ta fad'a.

     Kai kawai ta girgiza ba tare da tace komai ba taja hannun Nasreen ta fita zuwa d'aki.Tana zuwa ta tarar da missed call d'in Sameer bata jin zata iya calling back dan a yanzu bata son magana da kowa.

     Nasreen d'in ma kayan wasanta ta d'akko mata ta bata,ita kuwa kwantawa tayi kawai tana 'ko'karin mancewa da damuwar dake ranta.

                   ***
     Umma suna zaune a parlor Ahmad ya shigo,rissinawa yayi ya gaisheda ita ba tare da yana tsammanin amsarta ba.

    " Lafiya lau". Ta amsa ba tare da tana kallonsa ba.

     Zainab ma 'karfin hali tayi ta gaisheshi,yana amsata ya koma d'aki koh takan abinci be biba.

       Wajajen 11:15am sega Imran yazo,yana gaisawa da Umma ya komo wajen Ahmad.

       "Ya ake ciki neh yanzu?" Imaran ya tamabaya.

       "Ya kwa ake ciki ganinan na rasa abinda zanyi". Ahmad ya fad'a.

       " Yanzu ka samu ka kira su Aunty's nakan ba basu ha'kuri atleast za'a samu relief and maganar 'boye-'boyennan bashi bane ka rife ido kawai kaje gidansu ayi magana frankly kuskure ne an riga da anyi ba abinda ze chanja, hakane?"

        Kai Ahmad ya gid'a alamar "Eh".

        " Yaushe toh zakan?" Ya tambaya.

       "Today". Ahmad ya amsa.

         " Good".

    Ahmad bayan tafiyar Imaran ya kira Aunties nashi d'aya bayan d'aya ya basu ha'kuri.

     Da kansa ya shiga kitchen ya zuba abinci yaci ya komo d'aki.

    °°°
Se 11:16am Reyhana ta farka daga baccin dan bata san lokacin data soma ba.Yanzu taji d'an ded ba kamar d'azu ba ,seda tayi wanka ta shirya tukun ta sakko 'kasa.Ba kowa a parlor, kitchen ta shiga ta zuba abinci tukun ta dawo parlor ta zauna.

      Mommy da ta sakko ta ganta seda ta sake tambayarta dalilin kukanta amma ta'ki fad'a dan haka ta rabu da ita.

      Yau Nasreen dama ta samu se wasanninta take dukda bame taya ta kowa yana harkarsa.Walida tana d'akinta Ikram kuwa ta fita Bassam ma yana d'aki,Sageer da yanzu yama dena fitowa parlor balle cin abinci a table.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now