Page 21

174 13 2
                                    

       Zainab yanzu har ta saba ma kanta inde batai chatting da Ahmad ba bata jin dad'i,duk ranar friday kuwa seta kirashi sun gaisa.Umma har ta soma gano wani abun gameda Zainab dan ta tana lura da ita bata da zance sena Yaya Ahmad.

      Har pic d'insa ta saka ya turo mata wai duk sunan Umma ce zata gani dukda kuwa ba haka bane.Tun bata gasgata abinda zuciyarta ta fad'a yanzu ta yarda she fall for him.

                ***
Reyhana ce tsaye  hannunta ri'ke da yarinya ,a hankali ya 'karasa inda suke a tsayen.Koda ya isa wajensu ya tarar sun juya masa baya.

        "Reyhana". Ya kira sunanta cikin sanyin murya.

         A hankali ta juya fuskarta cikeda hawaye da nuna alamar damuwa.Kallonsa ya mayar kan yarinya ,a hankali ta waigo sede fuskarta ba komai(Hollow)

   A razane Ahmad ya farka,lokaci guda ya had'a zufa .Agogo ya kalla yaga 2:30am ,jikinsa a sanyaye ya shige bayi ya d'auro alwala ya tada sallah.

        Ko bayan ya idda sallar ya kasa komawa bacci,mafarkin da yayi ne yake ta masa yawo a kansa.

      " Koh wani abun ne ya faru?" Ya tambaya a zuciyarsa.

       "I have to call Reyhana  tomorrow morning".

        Wayarsa ya d'akko ya shiga gallery,photo na Nasreen tana baby ya bud'o yana kalla,hannu ya d'ora kan fuskarta yana shafawa a ransa yana ta sa'ke-sa'ke.Wayar na hannunsa bacci ya saceshi ,kan 'kirjinsa ya kifata ya soma bacci.

         Washegari da safe bayan yayi breakfast ya shige d'aki.Wayarsa ya d'auko ,number d'in Reyhana ya sa a wayar dan numbern ta baze goge a memoryn kansa ba.Da 'kyar ya samu yai dialing sede bata fara shiga ba ya katse.

      Kusan seda ya maimaita haka yafi sau hud'u amma sam baida courage yana tunanin ta ina zai soma magana kuma mey ze fad'a mata? Ya fad'a a ransa.

      Haka ya ha'kura da kiran ya ajje wayar gefe yana mey jin haushin kansa, da ace be d'au tsahon wannan lokacin ba da ba abinda ze hana ya kirata.

      Umma ya kira suka gaisa se sadiq shima dan sun kwana biyu basi waya ba.

               ***
Reyhana 'kawarta saudat ta haihu yau ake suna last two years tayi aure.

       Nasreen se tsalle take yau za'a unguwa da ita ta ishi kowa da maganar duk wanda ta gani seta fad'a masa Ummienta zata unguwa da ita dan Reyhana bata fiya fita unguwa da ita ba gara ma Mommy.
     
     
    3:30pm ta shirya ,itama Nasreen an shiryata tayi kyau sosai kamar a d'auka a gudu.

       Sallama sukai da Mommy suka fita.Ko barin layinsu batai ba mota ta tsaya yin duniya ta'ki tashi.

       Gashi Sageer baya gida balle ta kirashi ya kaita Mommy kuwa ta dena basu motarta.

      Tana cikin tunanin yadda zatai sega motar Sameer ta doso layin.

       "Shikenan kuma anace yazo". Ta fad'a tare da dukan steering motar.

        Aiko yana ganin motarta ya tsaya,yasan ko ya sauke glass d'in motarsa ba sauke nata zatai ba dan haka ya fito.

      Se da taga yazo daf ta zuge glass d'in.

       "Fita zaki ?" Ya tambayeta.

         Kai ta girgiza masa alamar "Eh".

        " Ok,but amma kamar motarki ya samu matsala koh?"

       "Eh amman zan samu napep". Ta fad'a dan karma yai mata tayi.

       " You don't need that,am here Reyhana senai dropping d'inki wajen da zaki". Ya 'kare maganar da murmushi.

ARZI'KI RABO(Completed)Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon