Page 31

225 25 0
                                    

Tana daga bakin 'kofar ta'ki 'karasowa gashi fitilar motar ta hasketa.

Fitowa yayi daga motar ya 'karasa har inda take a ransa yana tunanin mey ze fara ce mata.

"Reyhana am sorry ban kawo ta da wuri ba". Ya fad'a .

" Yanzun tana ina?" Ta tambaya.

"Tana cikin mota ,tayi bacci ne".Ya amsa.

Takawa tayi ta 'karasa inda motar take, ta bud'e 'kofar zata d'akko ta ya maida 'kofar ya rufe.

" Ka d'auke hannunka a 'kofar nan".Ta fad'a.

"We need to talk". Ya fad'a.

" Bani da wannan lokacin".Cewar Reyhana tare da watsa masa harara.

"Se yaushe ? Gobe? jibi? Yaushene zaki yarda dani ? Reyhana how many times do I have to tell you,kema kinsan ina nan bazan ta'ba d'aukan wannan tsahon lokacin ban zo ba ,ko bayan da na dawo kece kika hana ni zuwa you know why?" Cikin d'aga murya yake wannan maganar.

"Saboda na rasa abinda zance maki ki yarda dani a wannan lokacin,Umma tayi iya 'ko'karinta tazo amma mey ya faru ? Can you explain that?"

Reyhana shiru tayi ta kasa sake cewa komai ta kau da kanta gefe.

"Why are you punishing me like that ? am begging you please forgive me ,am very sorry!"

Bata ce masa komai ba , kasancewar ya d'auke hannunsa daga 'kofar motar hakan ya bata dama ta bud'e ,Nasreen dake kwance ta kinkimeta ta d'ora a kafad'a.

Bece mata komai ba ya bud'e 'kofar gidan gaba ya ciro jakar Nasreen ya mi'ka mata.

Hannu tasa ta kar'ba ta wuce,seda yaga shigewarta gida ya komo mota ya tafi.

Tana shiga gida ta kwantar da ita ,se lokacin taji sa'ida ba 'karamin dad'i taji ba daya dawo mata da ita.Se lokacin ta samu itama ta kwanta amma kuma se tuna muryar Zainab da taji d'azu take a wayar Ahmad,da wannan tunanin tayi bacci.

***
Washegari da safe bayan Nasreen ta tashi ta soma bawa Reyhana labari.

"Anty Zainab ce ta chanja min kayana". Nasreen ta fad'a.

" Jiya dama kaya ne a jakar ki koh ,shine kika hana a gani".

"Kuma ta d'aukeni a wayar ta". Nasreen ta fad'a.

"Kinci abinci jiyan?" Reyhana ta tambaya.

"Eh Umma ce ta bani ma". Ta amsa.

" Umma?".Reyhana ta tambaya.

"Eh Umman su Uncle ce ".

" Gidan Umma suka je kenan? Toh ko beyi aure ba daman?" Ta fad'a a zuciyarta.

Daga baya Nasreen ta shiga yin wasanta ta bar Reyhana da tunani.

°°°

Su Anty Asma'u yau Sageer ya kaisu gidansu Fatiman sa ,Mommy tana gida tana jiran su dawo taji bayani Abba sam besan da wannan batu ba.

Suna dawowa Mommy ta shiga tambayarsu ya aka 'karke.

"Matsalar daga kece Maryam". Anty Asma'u ta fad'a.

" Kamar ya ?" Ta tambaya tana neman 'karin bayani.

"Mahaifiyar yarinya tayi mana bayanin komai,tace dalilin daya sa suka guji Sageer shine sun samu labari ke bakya yarda 'ya'yanki si auri talakawa ,shiyasa suka ji tsoron abinda ze biyo baya kada daga baya azo ana da an sani".

ARZI'KI RABO(Completed)Où les histoires vivent. Découvrez maintenant