Page 6

215 22 0
                                    


Walida da ganin irin kallon da Mommy keyi mata yasa tace"Abune ya shigemin idon shine na sosa yayi ja".

"Ayya ya fita yanzu?" Abba ya tamabaya.

"Eh". Ta amsa.

Mommy kallonta tayi alamar kin ceci kanki d'innan.

***
Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa yau da dad'i gobe babu.

Reyhana tana d'aki tana nikke jera kayan data goge a wardrobe. Sallamar yaya Ahmad yasa ta fitowa dan wataran dama yana fita da key idan ya dawo ya bud'e base yayi knocking ba.

A sanyaye ya 'karaso d'akin." Sannu da dawowa".Reyhana ta fad'a.

"Yawwa". Ya amsa a sanyaye.

"Yaya wani abune?" Reyhana ta tambaya.

"Ahnn...kainane yake ciwo". Ya amsa.

" Ayya sannu kayi wanka sena zubo maka abinci kasha magani".Ta fad'a.

Tashi yayi ya rage kayan jikinsa ya shiga toilet,Reyhana kuma ta fita had'o abinci.

Sitting room d'in ya zauna yaci abincin kad'an -kad'an yake amsata.Paracetamol ta 'ballo masa ta bashi ya watsa,kan kujera ya samu ya haye yayi rigingine hannunsa ya d'ora kan goshi kamar me bacci amma ba baccin yake ba.

Reyhana kuwa bayan data kwashe kwanikan d'aki ta koma ta cigaba da abinda take dan tana tunanin ko gajiya ce tasa shiyasa ta bashi space.

Shikuwa ba abinda yake tunani se ta yadda ze 'bullo mata da wannan al'amari daya faru dashi.

Da asr ya tashi yaje masallaci bayan ya dawo kuma ya tarar tana kitchen had'a abincin dare saboda haka ya koma d'aki yana jiran anjima ya sanar mata.

Se bayan da suka kammala cin abincin dare sannan ya zauna da ita.

"Reyhana bansan ya zaki d'auki wannan abun da zan fad'a maki ba,ina me baki ha'kuri". Ahmad ya fad'a.

" Yaya mene ka fad'amin du na tsorata".Ta fad'a.

"Reyhana.. aa..an sallameni daga makarantar da nake teaching". Ya fad'a da 'kyar.

"Subhanallahi yaya meya faru? Meyasa?" Reyhana ta fad'a hankalinta a tashe.

"Director na school d'in ya fad'a mana cewa malaman school d'in sunyi masa yawa kuma biyan salary yana nema ya gagareshi and kuma yanzu sunfi son masu degree certificate".

Shiru tayi Reyhana hannunsa biyu ta ru'ko." Yaya addu'a kawai itace mafita ba damuwa ba jarabawace garemu,Allah ya musayya maka da wanda yafi wannan Yaya".

"Ameen". Ya amsa.

Sosai ta damu amma ta danne irin damuwar data shiga,ranar kusan dukansu basi cikakken bacci ba musamman Ahmad.

Ko washegari daya tashi yana d'aki ko breakfast d'in arzi'ki beba ya kwanta yana tunane-tunane.Reyhana ce ma take d'an kwantar masa da hankali da taga yana tunani seta zauna ta fara yi masa hirarraki kota kunna masu kallo da rana,haka da daddare dukansu tashi sike sallah.

Ko Umma be fad'a mata ba bayaso ta shiga damuwa,yanzu fafutukar neman abinyi ya tsindima.A rana seya fita yafi so uku,a haka har ya samu wajen aiki,sunayin sliding window.

A kullum ake biyansa kud'in ba masu yawa bana sede addu'a kawai.

Yau bayan fitarsa wajen 9am ko karyawa beba dan tashi sukai gas d'inma ya 'kare gashi ba kud'in refilling danma Allah yasa da 'yan wasu kud'i a hannunsa da Abba ya aiko mata sanda Sageer yazo.

Ragowar 3k ne dan haka da kanta ta fita bata da me aike.Ganin kayan abincin su sun 'ka'kkare ta sissiyo wasu abubuwan se ragowar ta d'uro gas.

ARZI'KI RABO(Completed)Wo Geschichten leben. Entdecke jetzt