Page 34

238 20 2
                                    

    Ahmad ya kasa cewa komai yana kallonsu,Reyhana wani kallon tara saura tayi mata tun daga sama har 'kasa sannan ta 'karasa bakin 'kofar ta bud'e ta shige cikeda ta'kama.

     Zainab baki ta saki taga 'karfa-'karfa,chak ta tsaya batada alamar shiga motar.

     Ahmad ne yai mata alama ta shiga baya lokacin da suka had'a ido ,seda taci 1min tukun ta shiga baya ta ra'be gefe haushi ya isheta.

    Shiru kowa yayi a ransu kowa da sa'ke-sa'ken da yake. A haka har aka 'karasa gidansu Reyhana ,yana parking ta fito daga motar ko takan Nasreen bata bi ba tasan dole ze d'akkota kuma da biyu tayi hakan dan ta sake ba'kanta wa Zainab.

       Bayan ya fito ya bud'e gidan baya ya d'akko ta ,tayi nisa ma da bacci.

      Zainab lokacin da taga yana fitowa daga gidan ta kauda kanta ta sake had'e rai,tunda ya shigo motar ya fiskanci hakan.

      "Ki dawo nan gaba". Ya fad'a.

       Yitai kamar bata ji ba seda ya sake maimaitawa tace.

        " A'a nan ma yayi".Ta fad'a muryarta ciki-ciki.

        "Zainab ki dawo nace".Ya fad'a wannan karan ya waiwayo.

        Bata sake cewa komai ba ta fita ta koma gaba tare da rufo 'kofar da 'karfi.

       " Fishi kike da Antyn taki?" Ahmad ya fad'a bayan ta shigo.

       "Anty ta". Ta maimaita tare da ta'be baki.

       "Ehmana ko kin mata ita Antynki ce?"

        Shiru tayi bata sake wata maganar ba tana kallon waje har suka  isa gida.

     Tunda suka shiga gida ta shige d'akinta takaici ya isheta.

                  ***

      Reyhana bayan tafiyarsa ta kai Nasreen d'aki ta kwantar da ita,tunani ta shiga yi na abinda ya faru,murmushi ta tsinci kanta tana yi ."Ko zata koma gaban oho mata".Ta fad'a a zuciyarta.

       Tana wannan batun sega kiran Ahmad ya shigo wayarta,yau a karan farko tayi picking.

      "Assalamu Alaykum". Tayi sallama.

       " Waalaikumussalam"Ya fad'a.

        "Ya jikin nata?" Ya tambaya.

         "Da sau'ki har yanzu bacci take". Ta fad'a.

          "Ok,toh idan ta tashi karki manta ki bata magani".Ya fad'a.

          " You don't have to mention dan bazan manta ba".Reyhana ta fad'a cikin sanyin murya.

      "Kina so kice kin fini damuwa da ita kenan" Ahmad ya fad'a.

       "Toh wa zai had'a ma". Cewar Reyhana.

        " Haka de kika ce ,itama ai ta sani".Ya fad'a.

        "Cabb! Waya fad'a ma nide kullum kodayaushe muna tare ko bacci baya raba mu".

      "Kwana nawa ne zan d'auke ta". Ahmad ya fad'a.

      " Ba inda zata".Reyhana ta fad'a.

       "In kina so ki zauna tare da ita seki biyo ta". Ya fad'a.

       "Hmm".

       " Hmm meh?"Ya tambaya.

        "Babu ,am hanging now". Ta fad'a.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now