Page 27

209 18 1
                                    

   Abba zaunar da Mommy yayi a d'aki yana tuna mata abubuwan da tayi wa Ahmad a baya.
 
      "Kinga de yadda ikon Allah yake koh?"Cewar Abba.

         Mommy shiru tayi bata ce komai ba tasan dama se ya dawo mata da zancen.

       "Shiyasa koyaushe nake fad'a maki ba wanda yasan gobe,yarannan ba irin abinda baki a kansa ba kika d'ora masa karan tsana ke seya saki 'yarki kuma bayan kindena ganin shi a gidanki nan ma ba'a tsira ba toh gashi ya dawo wajen 'yarsa".

     " Kai kuma dawo da zance baya duk abinda ya riga ya faru ai ya faru kuma meye amfanin tada zancen,maganar ya dawo ni be shafeni ba".Mommy ta fad'a cikeda borin kunya.

    "Tunatar dake nayi". Abba ya fad'a.

      "Wannan yaran fah baka ta'ba magana a kan halin dayake ciki ba". Mommy ta fad'a tana son chanja topic d'in.

    " Wa fah?" Abba ya tambaya yana neman 'karin bayani.

    "Sageer mana".Ta amsa.

     " Shi d'in kuma mey yake damunsa?"

      "Gashinan baya shiga cikin mutane abinci ma baka ganinsa ya ci aikin ma ni bansani ba koh baya zuwa".

     "Amma de ai shi ba yaro bane da za'a dinga jawo shi ana tambayarsa meke damunsa". Abba ya fad'a.

     " Toh zira masa ido zamu zauna miyi kenan koh me ze faru ya faru kenan". Cewar Mommy.

     "Ni kin ta'ba fad'a min idan ba yanzu ba?"

     "Toh yanzu ai na fad'a maka".

      " Toh Allah ya sawwa'ke".Ya fad'a.

      "Ameen". Ta amsa
 
                ***
  Ahmad daya koma gida zuciyarsa fyas ,Umma da Reyhana ne damuwarsa yanzu.

     8:13pm bayan ya dawo daga masjid ya d'auki wayarsa yai dialing numbern Reyhana.

•••

   Tana parlor a zaune ita da su Ikram da Mommy sega kira ya shigo wayarta.Sam bata kawo Ahmad bane dan ba layin data sanshi dashi bane.

     " Assalamu Alaykum".Tayi sallama bayan tayi picking.

     Seda yayi gyaran murya tukun ya amsa. "Waalaikumussalam".

      Da tana jingine da jikin sofa amma jin muryar yasa ta gyara zama." Kamar Ahmad ". Ta fad'a a zuciyarta.

   " Reyhana ".Ya kira sunanta.

     Tashi tayi tsam daga parlorn ta haye sama, su Ikram idansu 'kir akan ta bama su kad'ai ba hatta Mommy seda tabi bayan ta da kallo.

     " Waye?" Ta tambaya duk da kuwa ta gane mey magana.

     "Yanzu kin manta da muryar tawa ma?"

      "Da zaka fad'a min da wanda nake magana da yafi dan ina da abun yi". Ta fad'a.

     " Toh ranki ya dad'e ,Ahmad ne". Ya amsa.

      "Wane Ahmad d'in?" Ta tambaya.

      Dariya tambayarta ta bashi dan yanzun ya gano tasan mey magana sarai.

    "Reyhana please mana nasan kin gane mey magana,ina so miyi magana". Ya fad'a.

     " And nace a'a".Ta fad'a.

     "Please ,am very sorry". Ya fad'a.

     "Mey kayi min da zaka bani ha'kuri ?"

     "Laifi mana ,lokacin da ya kamata ace nazo ban..." Be 'karasa magana ba ta katse wayar

ARZI'KI RABO(Completed)Wo Geschichten leben. Entdecke jetzt