Page 16

178 15 0
                                    


       Gabaki d'aya yaran da sauri suka 'karasa wajen Mommy da ta kusa kaiwa 'kofar fita.

       "Mommy dan Allah karki tafi ki barmu". Walida ta fad'a tana ta'be baki zatai kuka.

      " Mommy please kar kiyi haka".Reyhana ta fad'a ta ri'ko hannun Mommy.

     Se lokacin ta kalleta ,Sageer ma 'karasowa yayi.

     Mommy dan Allah ".Ya fad'a muryarsa a raunane.

       " Sakeni".Mommy ta fad'a tana mata wani kallo.

       Reyhana a hankali ta sauke hannunta dan tasan duk dalilinta hakan ta fara.

       Suna ji suna kallo ta fita ,Walida take ta buga 'kafa tana ta kuka tana kiran Mommy.

       Abba da tun d'azu be kalli inda take ba duk da kuwa abun ya damesa sosai ,seda yaga ta fita ga Walida tana kuka.Fita yayi ,yaran zasu biyosa yace su tsaya.

      "Maryam". Abba ya kira sunanta.

      Yana 'karasawa inda take ya fisge trolley d'in daga hannunta.

      " Mey kike tunanin yi? Idan kin tafi ina zaki je"?" Ya tamabaya.

    "Gidan kawu na". Ta amsa.

     " Ki shiga ciki nace".Abba ya fad'a yana nuni da 'kofa.

     "Kusha zaman ku kaida yaranka muddin baze saketa ba ni kuma bazan dawo gidannan ba". Ta fad'a.

       " Adalci kenan ,ki raba auren yarannan?"

       Shiru tayi bata ce komai ba tana tsaye ita bata shiga motar ba kuma bata koma ba.

       "Ki duba kiga yarannan,haka zaki tafi ki barsu wani hali zasi shiga? Abba ya fad'a a sanyaye.

      " Nide na fad'a maka muddin na koma toh seya saketa".Mommy ta fad'a.

      "Muje ki shiga ciki". Abba ya fad'a.

      Tana huci tabi bayansa yaran suna kallo ta shigo da sauri suka je wajenta.

     Reyhana kuwa komawa tayi d'aki jiki a sanyaye. A zuciyarta tana tunanin mafita " Yanzu a kaina yau Mommy take 'ko'karin barin gidannan!" Reyhana ta fad'a a zuciyarta hawaye na gangarowa a idanuwanta.

               ***

   Umma tana komawa gida Ahmad ya 'karaso inda take.

      "Umma ta ha'kura Mommyn" .Ya tambaya muryarsa a raunane.

      Kallonsa kawai tayi amma ta kasa cewa komai.

      "Umma ki fad'a min". Ya fad'a.

      " Ahmad sede mu cigaba da addu'a ,Mommyn ta ta'ki amincewa mahaifinta ne de ya goyi bayanta ba". Umma ta fad'a.

     Labarin duk abunda ya faru ta zayyane masa,hannu yasa ya dafe goshi kansa yana sarawa.

     "Ha'kuri zakai Ahmad duk abinda kaga ya faru Allah ne ya tsara". Umma ta fad'a.

      Seda tayi da gaske yaci abinci kad'an koh fita ya 'kiyi,wayarsa ya d'auka bayan yayi sallahr zuhr yayi dialing number na Reyhana.

     Seda ta kusa katsewa tayi picking.

       " Reyhana ".Ya kira sunanta.

      " Uhmm".Ta amsa dan idan tayi 'kwakkwarar magana kuka zatai.

      "Reyhana dan Allah karki rabu dani ,bazan iya zama bake ba ina 'kaunarki Reyhana". Ya fad'a muryarsa na rawa.

      Jin haka yasa ta shiga kukan da take dannewa." Ahmad taya zanso na barka kaima kasan bazan so na rabu da kai ba".Ta fad'a.
    
       "I know Reyhana". Ya fad'a.

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now