Page 30

210 20 0
                                    

Ahmad beyi mamakin
'kin picking call d'insa da Reyhana ta'ki yi ba kusan daman an saba shiyasa be kawo komai a ransa ba.

Ita kuwa Reyhana ta kasa samin sukuni se tunane-tunane takeyi ,ranar batai cikakken bacci ba.

***

An d'auki kwana biyu Reyhana bata picking call d'insa text kuwa baya gajiya haka zeta tura mata tana ignoring.

Yau da safe tana shirya Nasreen se ro'konta take barta taje gidansu Anty Zainab.

"Ko zaki d'ige bazaki ba gara ma kidena tunanin zuwa". Reyhana ta fad'a.

Chono baki tayi tana buntsire-bintsire baki." Tashi mije kiyi breakfast ki tafi makaranta".Reyhana ta fad'a

"Toh". Ta amsa.

Reyhana ce ta fara fita a tunaninta ko Nasreen tana biye da ita.Ganin Ummienta tayi gaba tayi sauri ta bud'e wardrobe ta ciro kayanta kala d'aya ta cusa a cikin jakarta ta fito se muzurai take.

Mommy kafin ta 'karaso dinning d'in ta nufi d'akin Sageer.

" Yau ma bazaka aikin ba?"Ta tambaya.

"Zanje se anjima". Ya amsa.

" Toh ka fito kayi breakfast mana kai shikenan kuma se kaita 'buya a d'aki".

Da 'kyar ya taso,sake cin magani yayi dan ya lura da su Ikram kallon munafinci sike masa,daga ya had'a ido da Abba seya kauda kai.

"Nasreen ya naga jakarnan ta 'kara wani tudu mey kika sa aciki?" Walida ta tambaya.

Reyhana se lokacin ta lura da tudun jakar,hannu tasa tana shafawa ko zataji wani abun da sauri Nasreen taja baya.

"Ba komai fa". Ta fad'a kamar mey shirin yin kuka.

" Toh kiyi sauri ki gama ci kafin driver yazo".Reyhana ta fad'a.

Mommy da hankalinta baya gunsu ko tanka musu ma batai ba.

°°°

Mommy bayan ta komo d'aki ta kira Anty Asma'u ta sanar mata halin da ake ciki daga baya Anty Asma'u tace zata zo Sageer d'in ya kaita gidan itama ta gwada tata sa'ar.

Ahmad se bayan ya dawo gida ya tafi school d'in su Nasreen, lokacin daya je ba'a tashe su ba seda ya jira.

Tana ganinsu ta kyalla da gudu hadda tuntu'be.

"Uncle !" Ta kira sunansa.

"Uncle ita Anty Zainab bata zo ba yau?" Ta tambaya.

"Ehyyi". Ya amsa.

" Uncle ka kaini wajenta". Ta fad'a.

"Driver zezo ya d'auke ki ,ki bari se kin fad'awa Ummienki".

" Ai na fad'a mata ,kaga ta bani wasu kayan ma". Ta fad'a tana zuge zip d'in jakar.

Shide yasan Reyhana baza ta bari ya kaita gida ba.

"Ummienki bata san kin d'akko ba koh?". Ahmad ya fad'a.

" Toh dan Allah ka kaini ai bazan dad'e ba seka fad'a mata".

"Ince mata mey?"

"Kace mata ka kaini wajen Anty Zainab".

" Yanzu yamma tayi ki bari se gobe kinga ba school ma".Ya fad'a.

"Uncle dan Allah ka kaini". Ta fad'a tana bubbuga kafa kamar zatai kuka.

Seda ya d'an nisa tukun yace " Toh zan kaiki".

Tsalle ta shiga yi tana murna ,da sauri ta shige motar.Ahmad seda driver yazo d'aukansu ya fad'a masa Nasreen baza ta biyo su ba.

ARZI'KI RABO(Completed)Hikayelerin yaşadığı yer. Şimdi keşfedin