Page 25

174 23 1
                                    

     Duk cikinsu kowa ya kasa fad'ar koda 'a' ce ,daga cikin zuciyarsu kuwa tambayoyine iri-iri musamman Reyhana.

     Kamar 'kiftawar ido yaga taja hannun Nasreen sun shige mota,'ki'kam yayi be motsa ko ina ba kamar wani gunki.
   
       Nasreen cikin rashin nuna damuwa tayi ta waving bye ,cikin 'kan'kanin lokaci yaga wayam.Se a lokacin yayi 'kwa'kwarar 'kifta ido.

     "Meyasa ma na barta ta tafi?" Ya fad'a  a ransa.

      "Am stupid!" Ya daki saman motar.

       Gwiwa  ba 'kwari ya shige mota sannan ya bar gurin

       Reyhana da ikon Allah ta iya tu'kin motar dan hankalinta baya wajen,Nasreen da take mata hira ko sauraronta bayi take ba.Suna shiga gida taga Anty Asma'u da Mommy se maganganu suke suna kumfar baki.
  
        "Banda rainin hankali kai tsaye su sunzo ganin 'yarsu  bako tunani". Cewar Anty Asma'u.

         "Nasreen jeki d'aki gani ina zuwa". Reyhana ta fad'a da'kyar dan bakinta yayi nauyi.

      Ba musu ta wuce sama,su Mommy kuma lokacin sun bar hayaniyar da suke." Mommy meya faru?" Reyhana ta tambaya.

     "Yanzunnan 'yan uwan Ahmad suka fita ,saboda tsabar rashin kunya irin tasu wai gurin Nasreen suka zo harda wani tarkacen ledarsu sunan sunyo mata abin arzi'ki ca akai musu bata ci kowa irinsu neh mitsiyaci!"

    "Kuyi shekara shida baku waiwayi yarinya ba shine seyau ku kwaso tarikican 'kafarku kuce kunzo ganin yarinya". Anty Asma'u ta fad'a.

      Reyhana ta kasa cewa komai illa zame jiki datai ta haye sama dan kanta yana shirin bugawa ta rasa da wanne zata ji,ganin Ahmad koh zuwan wa'acen?

       Da'kyar 'kafafuwanta suka kaita zuwa d'akinta,a sanyaye ta zauna kan gadon Nasreen da har ta 'kwa'be uniform d'inta ,'karasowa tayi inda Reyhana take.

    " Ummie ki d'akko min kayan da zan saka".

     Sam hankalinta bayan gurun ta tafi nisan tunanin seda taji tana jijjiga mata kafad'a ta dawo hankalinta.

      "Ina zuwa ".Ta fad'a tare da mi'kewa ta bud'e wardrobe ta ciro mata.Nasreen tana gama sa kayan ta fita.

     "Shine Uncle da take magana? Meyasa se yanzu? may be aure yayi ya haifi wasu 'ya'yan shine ya tuna da Nasreen koh matarsa tasa yazo wajen 'yarsa ? Naughty brain nashi be fad'a masa abinda ya kamata ba seda.. No it can't be..what if yayi auren ai it's possible but...Ohh " Abinda yake ta mata yawa a 'kwakwalwarta kenan ,se yanzu kuma abunda su Mommy suka fad'a mata ya dawo mata.

°°°

Ahmad yana zuwa gida ya shige d'akinsa ya rufo 'kofa ,se yanzu yake daya sani.Tunani ya shiga yi koh ya kira ta a waya wata zuciyar tace"Kana gani koh magana bata had'aku ba a fili ma kenan balle waya".

     "Reyhana am sorry!" Ya fad'a a fili cikeda nadama kamar tana kusa dashi.

      Yana wannan tunane-tunanen har maghrib tayi be samu zuwa masjid bama se a gida yayi sallahr,se bayan ya idar da sallah tukun ya fita zuwa parlor.

         Umma tana zaune kujera fuskarta ba walwala shi be kawo komai a ransa bama,opposite da kujerarta ya zauna.

       Tunda ta amsa sallamarsa bata sake magana ba se yanzu.

       "Ahmad meyasa kayi min 'karya?" Ta tambaya.

       A razane ya d'ago da kai ya kalli Umma se lokacin ya kula da yanayinta.

     "Abinda kayi ka kyauta kenan? Ashe duk zaman da akai iya tsahon lokacinnan kusan shekara biyu kenan ni gani ka maida ni bansan mey nake ba koh? Ka janyo wa iyayenka wula'kanci da cin mutunci yanzu wa gari ya waya?" Se lokacin ta tsaya da magana.

      Yanzunne ya gane mey ya faru,Aunty's nashi sunje gidansu ,finally Mommy ta fad'a musu 6yrs rabonsa daya taka 'kafa gidansu Reyhana.

       "Ya Allah ka taimakeni". Ya fad'a a zuciyarsa.

    Ya bud'e baki zeyi magana Umma ta katseshi.

      "Ina tunaninka da iliminka ? Ha'k'kin 'yarka dayake a kanka duk ka mance ba ruwanka haka kake kuma jin dad'in bacci ni gani ka d'auke ni shashasha ashe kallon wawiya wacce batasan abinda take ba kake min ban isa na fad'a maka abinda zakai ba kai, gaka ka girma ka zama banban mutum koh? mahaifiyarka za kaiwa 'karya".

       Umma a rayuwarta ba abinda ta tsana kamar ai mata 'karya,gata da mita kuma idan tayi fushi se ansha wuya ake shawo kanta.

     Duk wannan fad'an da tai masa Zainab tana daga d',aki tana jiyowa ,ji take kamar ita akai wa fad'an sosai tausayin Ahmad ya kamata.

      Yana so ya bata ha'kuri amma ga mamakinsa se gani yayi ta tashi ta bar masa parlorn.

     Jiyai duniyar tayi masa zafi ya rasa inda zesa kansa, tashi yayi ya fita daga d'akin yana jiyo sanda ta banko 'kofar d'akinta,d'akinsa ya koma ya rasa mafita yunwar dayake jima ya dena ,wayarsa ya d'auka ya kira Imran ya fad'a masa duk yanda ake ciki ,nan yake fad'a masa gobe zezo suyi magana.

                ***

     Mommy tana ganin Abba ya dawo ta fad'a masa abinda ya faru ,a gaban idonta seya nuna mata bega laifinsu ba amma a ransa ba haka bane.

     Yau dinner d'in boring dan daga Reyhana har  Sageer ba wanda ya hallara ba, Mommy ma haka d'aki ta shige. 
 
       12:44am sam ta kasa bacci ga wani zafi da idanuwanta keyi ,tunanin  d'azu ta shiga yi fuskar Ahmad ta fara yimata yawo a kai.Canji kad'an taga yayi mata ,saje dayake kwance a fuskarsa se d'an murjewa daya 'karayi ga haske daya 'karu a  fatarshi.

      Bata ankara ba taji danshi a fuskarta ,ita kanta batasan dalilin kukan ba ,da tayi tunanin zata iya mance da rayuwar da sukai da Ahmad amma a yanzun taga ba haka bane komai ya dawo sabo.

      Ganin kukan baze mata magani ba ta tashi ta d'auro alwala ta tada sallah.

•••

  Washegari Saturday Nasreen ba school da wuri ta farka ta hana Reyhana komawa bacci gashi idanuwanta sunyi mata nauyi.

      "Ummie mije kitchen muyi indomie tare". Nasreen ta fad'a.

         " Nasreen please mana ga Aunty Walida ". Cewar Reyhana a kasalance.

          " Ai ita duka na zata yi idan na taso ta". Ta fad'a.

      Haka dole ta ha 'kura da baccin suka shiga kitchen.Labarin Uncle ta fara bata,chocolates dayake suyo mata.

      "Nasreen tun yaushe yake zuwa makarantar ku?"

      "Kullum kullum ya dad'e ,ya d'orani a lilo ya siyamin chocolate". Nasreen ta fad'a tana nishad'i abinta.

      Reyhana tunani ta tsindima ta mance da frying pan da ta d'ora a cooker gas ,seda taji 'kauri ta tuna da sauri ta dan'ki handle d'in hannunta ya goje ta 'kona d'anyatsa.

      " Arghh!" Ta saki 'kara.

     Takaici biyu ya isheta batasan sanda ta tsuguna ta soma kuka ba.

  °°°

    Zainab tun da ta tashi ta kasa fitowa,daga Umma har Ahmad tsoron had'uwa dasu take, tana tsoro kar ya huce a kanta,Umma kuma batasan ko har yanzu bata dena fishi ba akan abinda akai wa 'kannenta ba.

       Tana wannan batun ne sega Umma ta shigo d'akinta.

AR²💖

         1137+ words ,too short i know,please manage am not feeling well .
😤😷

Pls don't forget to vote.

Jasko💕

     

     

     

ARZI'KI RABO(Completed)Where stories live. Discover now