page 37

374 20 2
                                    

*بسم الله الرحمن الرحيم*

🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*MAKAUNIYA CE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸

By
Jiddah S Mapi

Page 37...
*___________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

Daddy ne yayi dariya yace "to masha Allah idan har abinda muke zargi a tsakaninsu ya tabbata to babu Wanda zai kaini farin ciki, domin ni na d'auki Hamma Yarda Kamar d'an Dana Haifa ne"

Baby tace "ai Daddy nima zanyi farin ciki matuka idan ta Aureshi sabida yanada hankali gashi kuma yana girmama na gaba dashi, kuma yanada fara'a"

Mommy tace "yanzu dai muyita Addu'a Allah yasa hakan ya kasance sannan mu  kara zuba musu ido, mugano menene a tsakaninsu, idan yaso kafin mutafi sai ayi maganar Aurensu ko?"

Daddy cikin fara'a yace "kwarai kuwa Hajiyata"

Minal saida ta gaji da gudun kafin tasamu wuri ta zauna tana naki, Hamma Yarda dariya yayi yakarasa wurinta yace "sorry Hajiya nasan kin gaji sosai kawo kopin nasa miki"

Minal had'e rai tayi ta kauda fuskarta gefe,
Cikin tsokana Hamma Yarda yace "shikenan tunda bakyaso ni bari naje na shanye"

Minal taso tayi fishi taki shan Nonon Amma yanda takeson Nonon yawuce misali, Turo baki tayi tace "gashi kasamin kad'an"

Kwashewa yayi da dry kafin ya d'iba mata, karb'ar kofin tayi ta d'aura a bakinta saida tayi Tass kafin ta sauke.
Haka sukaci gaba dazama agidan har sukayi one weak,
Acikin 'yan kwanakin Minal Nono kawai takesha, idan har batasha Nono ba tofa ranar akwai matsala, komin dare sai Hamma Yarda yaje ya nemo mata tasha kafin take iya bacci, Abun har mamaki yake baiwa su mommy, 'yammata kuma sai zuwa gidan suke wai sunason Baby da Minal suzama kawayensu, wani lokacin Inna ta korasu wani lokacin Baby tabasu numbarsu.

Hamma Yarda kuma yakamu da soyayyar Minal bana wasa ba, Sam bayason yaganta tayi tagumi zaije ya zauna agefenta yayi ta bata labaran dariya, har saita warware tafara dariya.

Ta b'angaren su Mommy kuma gani suke kamar Minal da Hamma Yarda suna soyayya, hakan ba karamin dad'i yayi musu ba,
Ita kuma Minal a matsayin d'an Uwa ta d'auke Hamma Yarda kamar yanda Baby ta d'aukeshi.

Yau da yamma su Minal suna zaune acikin gida bayan Minal tagama shan Nonone, taji zuciyarta tana juyawa, da sauri ta tashi tabar wajen mutane, Amai take shekawa tsakaninta da Allah, mommy ce takarasa wurinta tanayi mata sannu, Minal ciwon ciki take sosai, Rike cikinta tayi tana kuka, Mommy ce taji gabanta yana fad'uwa Dan ita tunda dad'ewa taso ta fahimci wani abun, innace ta karaso wurin tana tambayar Ko lafiya?
Ganin Minal tana amai rike da ciki itama taji gabanta yana fad'uwa, hannun Minal tariko tana kallo, da sauri tace Muga idonki Minal?
Minal da ta fita a hayyacinta ta mike tazo wajen Inna, bud'e idonta tayi tana dubawa, Innace tayi Salati cikin kuka tace "Shikenan wannan yaron ya cuceki Minal cikine dake".

Minal tayi baya baya zata fad'i da sauri Hamma Yarda ya riketa, ya d'auketa cakk sai d'akin Inna, A hankali ya kwantar da ita akan gado yana me tausaya mata, Baby ce ta d'ibo ruwa aka yayyafawa Minal da karfi tasaki ajiyar zuciya, hawayene yafara bin fuskarta masu d'umi, Mommy ce ta riko hannunta tace " kidaina kuka idan Allah ya yadda bazaki zauna da cikin nan ba, dolene azubar dashi".... Da sauri Inna ta katse Mommy tace "bakida hankaline Maryam? Wani irin magana kike? Kinsan hukuncin Wanda yazubar da ciki kuwa? To kul karna sakejij kinyi irin wannan maganar koda wasa"

Mommy ce tace "kiyi hakuri Inna bazan karaba insha Allah to amma ina tunanin idan har mutane suka San ta haifi d'a ba Aure wazai Aureta?"

Hamma Yarda ne yace "ni zan Aureta Mommy"

MAKAUNIYA CE Where stories live. Discover now