Part 3

143 13 1
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...?*
_GUGA YA HANA_

*MALLAKAR:-OUM MUMTAZ*

*WATTPAD@ Oum-Mumtaz123*
*INSTAGRAM@itz_me_real_oum_mumtaz*

*charpter 3*

********Hausawa suka ce mata da miji sai Allah,wanda hakan take,domin kuwa Abba da Mami tare suka fito suna murmushin su suna zuba k'amshi alamun sun riga da sun shirya abin su tintini(na ciki na ciki),falon da suke zama tsakanin su iya ya su suka wuce inda suka tar da Zulaykha cikin shirin wani mini skirt bakid'aya tsaya mana a guiwarta,sai kuma rigarta long sleve da ya matikar mata cas-cas da ita sai baza k'amshi take yi kanta ko d'ankwali babu kamar yadda take zama idan tana gida sai dai ta raba gashin kan nata gida biyu da ke samun gyara sosai ba kad'an ba.

Game nata na candy crush take bugawa kamar wata irin yar tsana saboda yadda take yarintar tata ba zama mutum ya ce ta kai 24yrs ba sai irin 19-20,murmushi take ta faman dokawa alamun sosai game din ke tafiya da imaninta.

"'Yar Abba har an fito kenan"? Mami ta fada a lokacin da take ma kanta mazauni akan kujerar da Abba ya zauna yana kallon 'yar tasa kuma abar k'aunar tasa fuskarsa shimfid'e da murmushi saboda yadda ta masa kyau sosai ba kad'an ba kamar mahaifiyarta.

"Sannunku da fitowa" ta fad'a ba tare da ta d'ago kanta ba saboda yadda game d'in ya tafi da imanin ta bakid'aya,agogon da ke manne da bangon falon Mami ta kalla wajen biyar da rabi amma har yanzu shuru Musty bai iso gida ba,a ranta tana fatan Allah ya sa lafiya.

K'amshin turaren da suka ji ne ya tabbatar masu da wanda ya shigo tun kamin ya yi magana,"Mamina na dawo" Musty ya fad'a a lokacin da yake ma kansa mazauni akan kujerar da Zulaykha ke zaune na 3 seater.

Hararar wasa Abba ya aika masa ya ce "Wato kai kuma Mamina ka kawai ka gani ko Babana?" Sosai kai Musty ya yi cike da jin kunya ya ce "Afuwan Abba wallahi ba haka ba ne."

"Aishatu ji min ja'irin yaro idan ba haka ba to mene ne?" Abba ya fad'a yana sakin dariya saboda yadda ya ga Musty na ta faman sussunne kai kamar wanda ke gaban sirikinsa,ita ma Mami dariyar ta yi kawai ba tare da ta ce komai ba tana bin dan nata da wani irin kallo k'asa-k'asa ba tare da su Abba da shi kansa Mustyn sun lura ba.

Ihu Zulaykha ta sake kamar wata k'aramar yarinya tana faman burburwa a wajen d'aya su yin kanta bakid'ayansu,suna tambayarta lafiyarta kuwa? Duk hankalinsu ya tashi saboda yadda ta bi ta birkice masu.

Sosai ta sake masu kukan shagwaba harda gulmammun hawayen ta da ya sa Abba sake rikicewa yana kokarin tarota don kar ta fad'i. Sai da ta bi ta gama daga masu hankali bakid'ayansu kamin ta tsagaita da borin da take musu tana binsu da kallo daya bayan daya,inda ta ga fuskokin su duk cikin tashin hankali da ya sa ta fashewa da wani irin dariyar shak'iyanci da ba ko yaushe take yi ba tana faman nuna su da dogin yatsunta masu kyan gaske.

Wani irin tukukin takaici ne ya tokare ma Mami wuya saboda ganin yadda Zulaykha ke k'ok'arin raina masu hankali kamar ta ga wasu mahauka ta cike da hasala ta ce "Amma ke dai an yi sakarar yarinya wallahi!! Ai wannan naima kike k'i d'aga mana hankali da yammar Allah kuma ki samu a gaba kamar wasu sa'annin ki kina yi mana dariya saboda kin raina mana hankali?"

Tsagaitawa da dariyar Zulaykha ta yi tana kwabe fuska kamar za ta fashe kan an ce mata sakarar yarinya! Harara Abba ya watsa ma Mami ya ce "Akan wani dalili za ki ce ma Mamana sakarar yarinya? Allah fa idan ba ki kiyaye ni ba akan Mamana ranki idan ya yi dubu saina lalata shi Aishatu! Haka kawai yarinya da gidan ubanta ki bi ki hana ta sukuni ki ce ba za ki bar ta ta yi abin da ta ga dama ba! Ki daina mini irin wannan idan kina so mu shirya wallahi."

Sosai ran Musty ya 'baci akan abinda Abba yayi ma Mamin sa duk akan Zulaykha amman haka nan ya boye nasa bacin ran ya ce "Abba ka yi hak'uri dan Allah,kuma ke ma Mami ai bai kamata akan wannan karamin abin sai kin tanka ba,ko ba ki ga cewa har yanzu ita Ummin yarinya ba ce kuma kike k'ok'arin biye mata akan wannan k'aramin abin ba?"

Mami ba ta sake magana ba saboda ganin yadda d'an nata ke mata ido alamun karta sake magana, Abba kuma gefen Zulaykha ya zauna da ta fara matsar kwalla ya ce "Me ya sa me ki ne kike kuka Mamana?" Ya yi maganar cike da rarrashi!

Da ya sa Zulaykha turo ba ki ga ba ta ce "To ni Abba ba fad'uwa na yi a game dina ba." Sai kawai Abba ya yi dan dariya ya ce "Gaskiya waya ba ki kyauta mana ba da kika sa Mamana ta fad'i wannan game da ni d'in,amma dai sai na yi maganin ka."

Haka nan Abba kwatakwata bai ganin laifin 'yarsa akan duk wani abin da za ta aikata kai kyau da akasin haka da ya dasa ma Mami tsanar yarinyar har cikin zuciyarta.

Sosai Abba da Zulykha suka shiririce Abba na tarairayarta ita kuma tana zuba masa shagwa'ba son ranta har ma sun manta da Mami tare da Musty da ke cike taf a wajen saboda ganin yadda Abba yake masu rashin mutunci akan yarsa,haka nan suka wuce d'akin shi musty din dake da nasa side d'in daban kamar za su tashi sama.

********Mik'ewa daga durk'ushe da yake ya yi yana sharar kwalla na tausayin kansa da kuma ita karan kanta matar tasa da ke k'ok'arin aikata abin da za ta iya da-na-sani zuwa gaba.

Da kansa ya shiga madafar tasu duk da irin tarin da yake yi saboda rashin sabo ya k'arashe girkin duk da bai wani iya sosai ba ya kashe itacen tare da kau da abubuwan wurin ya mai da su mahallinsa kamar yadda yake ganin Alina na yi a baya.

Gwanin tausayi haka nan ya share gidan nan tas tare da wanke duk wasu kwanikan da ke wurin saboda kawai ya faran tama gimbiyar tasa rai,ya daibo ruwa a can borehole da ke unguwar tasu ya ciccika duk wasu kayan amfanin na ruwa sannan ya sauke nannauyar ajiyar zuciya ya shige d'akin nata,bacci ya tadda ta na yi akan katifarta da ke lailaye da zanin gadon da ya sha ruwa a duniya sosai.

Bai tashe ta ba ya cire kayan jikinsa sannan ya wuce bayi ya yo wanka,kamin ya shirya cikin wani kayansa na yadi da shi ma daga gani ya ga duniya amma kuma a wanke suke tsaf ya yi sallah na azahar da ta kufce masa,bayan ya idar shi ma ya cire rigarsa hadi da hayewa kan gadon ya fuskanci fuskar matar tasa da ke baccinta hankali kwance ya tsira mata ido cike da tsantsar soyayyarta ya fad'a tunanin rayuwarsu ta baya kamin akai ga wannan matsayin.

********"Hmm mai ake ciki ne yanzu akoi wani motsi ne?" Mami ta tambayi Musty da ke zaune bakin luntsumemen gadon nasa ransa na matik'ar tafarfasa kamar ya yi fiffike ya je ya kakkarya Abba kowa ma ya huta akan Zulaykha.

Ajiyar zuciya mai k'arfi ya sauke kamin ya janyo wayarsa da ke kan side bed drower ya ya yi danne-dannen sa cikin mintuna uku Mami ta ji karan sako a wayarta da ke hannun ta,alert ne na zunzurutun kud'i kimanin naira million biyar Musty ya yi ma mahaifiyar tasa transfer,nan take kuwa ta naimi duk wani bacin ran da ke tattare da ita ta rasa ta fara zunduma masa albarka kamar babu gobe.

Part nasu ta wuce bacin ta saita fuskarta kamar babu abin da ya faru suka yi kici'bus da Abba da ya fito da niyyar tafiya masallaci ta yi masa a dawo lafiya ta yi wucewarta d'aki ba tare da damuwar komai ba.

Bangaren Zulaykha kuwa gani ta yi bak'on ta ya zo da magriba,wanda hakan ya sa ta sake yin wani wanka ta tsaftace jikin ta sannan ta fito zuwa harabar gidan nasu da hasken lantarki ya yi masa k'awanya kamar rana,k'ark'ashin wata rumfa ta yi ma kanta masauki kan wata grasses tana kallon sararin samaniya kamar mai tunanin wani abu.

Wasu ma'aikata ne maza dake daga can wurin gate ke zaune kan benci su ukun su suke hirar su,ganin fitowar Zulaykha ne ya sa su mai da akalar hirar tasu akan gulman mai gidan nasu wato Abba da kuma 'yarsa akan rashin adalcin da suke tafkawa a gidan da kuma inda suke aiki mana k'asa da su.

*vote*
*comment*
*share*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now