Part 24

67 8 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...!!*

*©️OUM_MUMTAZ✍️* 

_WANNAN LITTAFIN TIN DAGA FARKON SA HAR K'ARSHEN SA NA SADAUKAR DASHI GA ~MSS FLOWER🌸🌸~ MARUBUCIYAR :_
~LAFAZI~
~AR SO~
~SARKI~
~GUMBAR DUT'SE~
_SON SO FISABILILLAH❣️💃🥰❣️❣️_                            
   

           *Charter 24*

******** YUSUF SHUWA. Shine cikakken sunan mahaifin su d'an asalin garin Kaduna tare da matar sa ASMA'U da suke k'iranta da UMMA.

Suna da rufin asirin Allah dai-dai gwargwado,domin kuwa basu naimi ci,sha ko sutura da kuma buk'atun yau da gobe sun rasa ba,sana'ar Yusuf shuwa tin tasowar sa itace saida kayan masarufi a cikin kasuwar garin Kano.

Shekarar auren su guda suka haifi d'an su na fari da yaci sunan mahaifin baban sa ZULAYM,tin daga nan kuma basu sake samun wani cikin ba,har sun fidda rai da sake samun wani haihuwa kwat'sam saiga wani cikin a lokacin da Zulaym yakai 19yrs,wanda yake shekarar sa ta 20 cif cif aka haifo masa k'ani da yaci sunan baban maman sa wato AHMAD.

A lokacin ne akayi ma YAYA aure tare da wata y'ar uwar sa mai suna HAUWA'U da shi kuma Ahmad kan k'irata da HAJJA,don haka sai sunan ya zamana kowa ya santa dashi harma Hauwa'u d'in ya bace.

Hajja tare da surukar tata wato UMMA da kuma mahaifiyar ita kanta Hajja d'in mai suna HIDAYA tare suka samu ciki a lokaci guda.

Ahmad na da 5yrs Umma ta kuma haihuwar wani d'a namijin da yaci suna IBRAHIM suna kiran sa da HIMU.
Hajja ma d'a namiji ta haifa da yaci sunan mahaifin mijin nata wato YUSUF(dad) kenan.
Sannan mahaifiyar Hajja kuma ta haifo d'iya mace da taci suna KAUSAR,a wajen haihuwar kausar d'in mmn Hajja ta rasu,don haka sai Hajja d'in ta hade dan nata wato Yusuf da kuma k'anwarta Kausar take kula dasu amma bata shayar da ita.

Daga kan HIMU kuma UMMA bata sake haihuwa ba,don haka sai suka tattara kulawar su baki daya kwacokan akan yayan nasu,yara kuwa sun taso ne cikin t'sant'sar k'aunar junan su fiye da tunanin mai karatu,YAYA shine sunan da suke k'iran Zulaym babban yayan su dake matik'ar kulawa da k'annen nasa fiye ma da yadda mahaifin su zai kula dasu.
Hajja ta sake haihuwar d'a namiji sunan sa AHMAD shima suna k'iran sa da AMADU,Bayan shekaru ta sake haihuwar wani d'a namijin da yaci suna JAFAR.Wanda cikin wanna shekarun kuwa abubuwa da dama sun faru,ciki harda rasuwar YUSUF wato baban su HIMU.

Sosai kuwa mutuwar tasa ta matik'ar girgiza su a wannan lokacin,amma da shike sudin musulman kwarai ne,kuma sun yarda da fad'in ubangijin mu kan _KULLI NAFSIN ZA'IKATIL MAUT_ sai suka d'auki dangana suke binsa da addu'oin dacewa.

Cikin hakan kuwa harda girman su Kausar,inda UMMA da kanta ta hada auren AHMAD(maibin bayan yaya) da KAUSAR. Kuma Alhamdulillah zaune suke lami lafiya.

YUSUF(Dad), AMADU da HIMU tare Yaya ya kaisu makaranta acan garin Zaria daga cikin Kaduna , AHMAD dama ya rigasu zuwa don haka tin kamin bikin sa da kausar ya kammala nasa karatun,sai ya zamana YUSUF,HIMU da AMADU ne kawai ke can makarantar.

A lokacin Jafar yana k'arami sosai domin ko bai wuce 4-5yrs ba,kuma a lokacin ne KAUSAR ta haifo d'an ta na fari kyakkyawa son kowa k'in wanda ya rasa,ranar suna na zagayo wa yaro yaci sunan Yaya wato ZULAYM suna k'iran sa da YAYA shima kamar yadda takwaran nasa ya buk'ata.

Wanda kuma dama shekarar da ta gabata HAJJA ta sake haifo diyar ta mace mai suna KHADEEJA abokiyar fad'an Yaya k'arami.
Da shike tazarar shekara guda ne t'sakanin YUSUF da AMADU tare suka kammala makaranta dikkan su uku.

Acan Zaria d'in inda sukayi makaranta YUSUF da AMADU suka samo matan auren su da suka kasance wa da k'anwa FATIMA(mum) da MARYAM(um-asmy).

Anyi aure an gwangwaje lafiya kalau inda suka tare da amaren su acan garin Abuja,dikda kasuwan cin takalma da shi yusuf d'in kanyi acan kano.

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now