Part 29

61 8 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...?*

*©️OUM_MUMTAZ* 

_WANNAN LITTAFIN TIN DAGA FARKON SA HAR K'ARSHEN SA NA SADAUKAR DASHI GA ~MSS FLOWER🌸🌸~ MARUBUCIYAR:_
~LAFAZI~
~AR SO~
~SARKI~
~GUMBAR DUT'SE~
_SON SO FISABILILLAH❣️💃🥰❣️❣️_                          
   
           *Charter 29*

******** B'agaren Mamy da Musty kuwa tin da suka dawo gida banda kuka da kaicon ta babu abinda Mamy keyi,wanda kuma Musty ya gagara bata hak'uri, banda zuba mata idanu babu abinda ya iya yi. Tabbas ance uwa ta wuce gaban kowa,wanda ba don haka ba da yau babu abinda zai hana ya faffala ma wannan matar data kaisa ta baro.....

Cike da bak'in ciki gami da takaici cikin chunkushashshiyar murya yace, "Nifa ba kuka nasa kizo ki zauna kiman ba!!! Shiga d'aki zakiyi ki fiddo da dik wasu kud'ad'en da kika san ina kawo maki tinda dama ba amfani muke dasu ba,sabida babu abinda muka naima muka rasa cikin gidannan,kwad'ayi ce kawai take sa muke kwasan kud'ad'en bayin Allah da suka sako mu inuwa"

Sharce majinar dake sauk'o mata tayi ba tare da tayi magana ba ta mik'e zuwa d'akin ta,few minute ta fito daga d'akin hannun ta rik'e da wayarta ta samu guri ta zauna.
Cikin mintuna da bai wuce guda goma ba ta juye ma Musty kud'ad'en cikin account nata tas babu ko d'igo zuwa cikin nasa cike da wani irin nadama mara misaltuwa.

Haka nan suka kwana cikin rashin dad'in rai,washe gari da sassafe wajajen k'arfe takwas Musty ya tafi station akayi masa iso wajen DPO,wanda dama anyi dik wasu lissafe-lissafen daya kamata tin jiya babu ragin ko k'wandala hakkin mutane a cikin account nasa sai halalin sa da yake d'auka na salary nasa kamin yaji kamar an sauk'e masa wani gundumemen dut'se daga t'sakar kansa,har wani fresh air yake ji yana shak'a.

Gida ya wuce inda ya tarda Mamy cikin shirin zuwa asibiti domin dubo Ummi d'in da suka kwana acan,harda girki kuwa mai rai da lafiya ta masu,da yaso yak'i zuwa amma ta tursasashi,sabida su wanke bak'in fentin da suka lafta ma kansu! Wanda suka tarda jikin ma da sauk'i,amma daga ita har Abbah babu wanda ya sakar masu fuska hakan yasa jikin Mamy sake yin sanyi,wanda suka zauna jugum-jugum sai ga Dad tare da MUM da kuma Jiddah sun zo su da kayan breakfast suna tambayar ya mai jiki,sai kuma a lokacin suka saki fuska harda cin abincin da su Jiddah suka kawo wanda ko kallon na Mamy babu wanda yayi idan aka d'auke Anty Khadee da taji Mamyn ta bala'in bata tausayi sbd yadda taga uban zabgewar da tayi cikin kwana guda.

Shi kam Musty yasan tabbas yayi ma kansa,kan soyayyar da yake ma Ummi yasan idan ba wani ikon Allah ba kam tabbas shi da ita saidai hange daga nesa.
Wajajen azahar aka sallamo su suka dawo gida,wanda aka sake yin zama na musamman tare da Dad da ya sake tausar zuciyar Abbah,tare da yima Mamy da kuma Musty nasiha mai rat'sa jiki daya sa wani nadamar sake rufta masu,inda Allah ya taimaka ma Dad ba irin mutane masu baki sakaka bane,don haka babu wanda yasan abinda ya faru idan aka d'auke way'anda abin ya shafa.

Har k'asa Musty ya duka ya sake basu hak'uri akan abinda sukayi masu shida mahaifiyar sa,suka kuma tabbatar mashi da sun yafe masu har cikin zuciya kamin aka wat'se zuciyoyin su wasai amma banda Musty da tunanin ta yadda zai had'u da dangin mahaifin sa yake ta faman k'ullawa da kwancewa.

...……...

"Ni dai wallahi yau sai naje wajen Anty Khadee Ammah nah"  Waleed ya fad'a cikin b'ata fuska cikin marairacewa kamar ya fashe da kuka yana faman cuno baki gaba.

Tagumin da Ammah tayi ta janye cikin gajiyawa da magiyar da Waleed d'in ke mata tin ranar dasu Jiddah d'in suka tafi tace, "ka fita fa daga ido nah kamin na sab'a maka a gidannan ko?"

Ai kuwa kamar jira yake irin k'ananun yaran nan ya fashe mata da kukan iya hege yana ta faman tirje-tirje da k'afafuwa!!

Wawuro maficin dake gefen ta tayi,da yasa shi ficewa da gudun sa yana shidai sai yaje gidan Anty Khadee ko ayi yak'i yau a gidannan!

Kicib'us sukayi da Yaya da yanzu suke rafka sallama tare da Husnah da matashin cikin ta yayi mata das dashi suna baza uban k'amshi abinsu gwanin birgewa!!! Dakatawa daga biyo Waleed d'in Ammah tayi tana murmushi cike da jin dad'i tace, "Maraban ku da zuwa..."

Da d'an sassarfa Husnah ta k'arasa zuwa wajen Ammah d'in ta fad'a jikin ta da yasa Ammih fitowa daga d'akin ta tare dasu Mima sabida jin hayaniya a t'sakar gidan nasu!!!
Wanda hakan yasa suka kaure da hayaniya cike da farin ciki suna masu oyoyo,wani irin farin ciki ne ya kama zuciyar Yaya sbd ganin yadda gidan nasu ya koma happy family kamar baya!!! D'akin Ammih suka wuce,Waleed na lik'e da Yaya yana kora masa rok'o kan dan Allah su tafi tare dashi yana son zuwa gidan Anty khadee wajen Nuraaz!!!

Nan suka wuni suka shiririce abin su gwanin birgewa har zuwa yamma da Babi ya dawo aka zauna dashi shima suka sha hirar su,sai can bayan isha'i kamin suka tashi tafiya,da yasa Waleed tada masu bori don dole aka tafi dashi tare da Hamad da shima yace sai ya bisu!!!

Gidan Dad suka wuce,da suka samu tarba ta musamman dikda basu san da zuwan nasu ba,su Hajiya Jiddah sai faman surutu take zuba masu wanda saida Yaya ya kora ta kamin suka sami lafiyar kunnen su,a lokacin wajajen k'arfe tara na dare ne,don haka sai kawai Yaya ya wuce dasu gidan sa baki d'aya kan gobe idan yaso sai suje mata sabida yanzu babu dad'i dare yayi sosai,ba don sun so ba haka suka bishi sabida sanin halin sa na rashin maimaita magana idan ya fad'e ta!!!

"Akoi wata kyakkyawa dana gani yasin ta fiki had'ewa Anty Husnah!" Waleed ya fad'a cikin shek'iyanci a lokacin da suke zaune parlo wajajen goma na dare! Harara ta wat'sa masa batare data basa ansa ba Hamad yace, "ba wani nan,ni ban tab'a kallon wacce takai Anty Husnah kyau ba,bamu son fyori!!"

Ai kuwa wani irin want'salowa gaban Hamad Waleed yayi,cikin son tabbatar masa da abinda yake fad'i yace, "Wallahi da gaske nake,kardai kace man har ka manta da Anty mai kyau d'innan na ranan??"

Shiru Hamad yayi alamun son tuno wacce Waleed d'in ke kira da Anty mai kyau amma ya gagara tunowa.
Gyara zama da kyau yayi yace, "Wai har yanzu baka tuno da wannan wacce suka je gida da Anty Jiddah ba har suka kai bayan la'asar da muka sha game da wayar ta?"

Ai kuwa shima gyara zama yayi mai kyau yace, "Ayyooo!!! Ai saika man bayani ta yadda zanfi saurin tafiya gana kai kuwa,ba wai kana yiman kwane-kwane ba!!! Ai kuwa tabbas wannan kam k'arshe dama zan samu ire-iren su su zan zuba guda hud'u reras idan na tashi yin aure nah wallahi"

Yaya da tinda suka fara magana ko kallon su bayyi ba,balle kuma yasa masu baki ya d'aga fararen idanun sa fes ya sauk'e kan fuskar su cikin t'sare gida sabida jin bayanan da suke,ai kuwa nan take dik sukayi mit kamar babu su a wajen suna t'sili-t'sili da idanuwa! Girgiza kai kawai Yaya yayi cikin d'aure fuska tamau yace, "Ku wuce kuje ku kwanta kamin na tattaka ku a gidannan!!!!"

Ya k'arashe maganar cikin kakkausar murya da yasa su bajewa lokaci guda har suna rige-rige sabida sanin halin sa t'saf zai mazge su idan ya mik'e!!!!

"Yaya wai akoi wacce tafi ni kyau???" Husnah ta fad'a tana mai narke masa cike da wani irin abu mai d'aci dake taso mata can k'asan zuciyarta tinda Waleed ya d'auko maganar Anty mai kyau da bata ma santa ba ita kam.

Murya can k'asa-k'asa ya rad'a mata cikin kunnen ta yace, "karya suke,kaf cikin duniyar nan babu wacce takai My Ma'u kyau" wanda hakan yasa ta lumshe ido cike da t'sananin jin dad'i ta wulla bakin ta cikin nasa suka fara aika ma da junan su zazzafan sak'onni cike da t'sananin shauki da kuma begen junan su.

*vote*
*comment*
*share*
  
*OUM MUMTAZ✍🏿*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now