Part 28

84 9 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...?*

*©️OUM_MUMTAZ* 

_WANNAN LITTAFIN TIN DAGA FARKON SA HAR K'ARSHEN SA NA SADAUKAR DASHI GA ~MSS FLOWER🌸🌸~ MARUBUCIYAR:_
~LAFAZI~
~AR SO~
~SARKI~
~GUMBAR DUT'SE~
_SON SO FISABILILLAH❣️💃🥰❣️❣️_                          
   
           *Chapter 28*

******** A lokacin da y'an sandan suka k'arasa gidan Abbah d'in ba k'aramin b'arna suka tarda ma'aikatan sukayi ma gidan ba,sabida hatta ga windows na motocin sun faffasa cike da t'sananin fusata da yasa Mamy kanta gagara fitowa tayi ta kulle kanta a d'aki tana zuba zawo na tashin hankali,ita kam Anty Khadee banda addu'ar neman t'sari kan wannan haukar tasu babu abinda take cikin d'akin ta tare da fatan Allah yasa kamin yaran ta su dawo daga makaranta su Abbah su d'au mataki gudun kar a illata mata su (uwa mai dad'i,a dik halin da take ciki kyakkyawa da mummuna to kuwa tabbas bata tab'a mancewa da abinda ta haifa😘).

Da k'yar suka samu nasarar dakatar dasu ta hanyar fet'sa masu tiyagas suke kame su,suna antayawa cikin motocin su tas suka kwashe su hatta ga mai gadi suka gark'ame su kamin Mamy da Anty khadee dake a t'sure har yanzu suka firfito suna zare ido!!!

Wanda saida suka tabbatar da sun kwantar masu da hankali kamin suka tafi da yaran bayan sun d'auki dik wasu bayanan da suka kamata,suka kuma bar masu wasu y'an sandan guda biyar a bakin gate da zasu kula da masu shige da fice zuwa wani lokacin idan k'ura ta lafa.

A cikin wannan yanayin su Abbah suka iso,wanda su Aymana ma already sun dawo gida dama,wanda hakan yasa Abbah tare da Dad basu wani zauna ba,sallah kawai sukayi ko cin abinci basu yi ba suka wuce station tare da su Mamy baki d'aya da taso zille ma tafiyar.

Inda suka tarda harda Ummi dake zaune kan kujera kanta k'asa zuciyarta kamar ta faso k'irjinta sabida jin laifin toye hak'k'in ma'aikatan ta da ake tuhumarta da shi tinda aka kawo ta station d'in ta gagara magana!!! Sai uban kuka da take sharb'a kamar babu gobe sabida bak'in ciki da takaici.

Banda wani irin mummunar kallo babu abinda Abbah ke wat'sa ma Ummi tin wajen zaman da aka basu da suka k'araso cike da t'sananin jin haushin ta,da kuma takaicin dake cin zuciyarsa tin-tini!! Mamy na zaune wajen t'sam kamar t'summa a randa k'yat take jira ta fesa da gudu sbd yadda k'irjinta ke dukan uku uku sbd tasan mai ta aikata,ga kuma Musty da shima ke zaune rik'e da kansa ya rasa maike masa dad'i kwata-kwata,wani irin nadamar biye ma hud'ubar mahaifiyarsa ne da kuma d'acin ta ke taso masa daga can k'asan zuciyarsa kamar ya mutu ya huta don bak'in ciki da kuma takaici.

Dad nada niyyar ficewa ya wuce gida tinda abin kamar family issue ne amma Abbah ya buk'aci kan ya zauna babu damuwa.
Biyu daga cikin ma'aikatan kamfani da kuma biyu daga cikin ma'aikatan gida mata biyu da maza biyu da zasu wakilci y'an uwan su aka ciro daga cell zuwa gaban Cm_p domin aji ba'asin wannan masifar.

……...……

Wani irin shiru cikin station d'in ya d'auka a lokacin da way'annan bayin Allah suka gama koro bayani dalla-dalla aka rasa wanda zai fara bud'e baki t'sakanin Abbah da UMMI banda ido da suka sakar ma Musty dake jin kaf duniya babu wanda yakai sa muzanta a yau d'innan!!!

"n.i..ce nas...s aka rage Albash...in su Ya Musty...?" Ummi ta fad'a cikin rawar murya dake tafe da wani irin hargit'sat'st'sen kuka mai matik'ar tab'a zuciyar mai sauraro!!

"Tabbas nid'in a yau na nuna ma duniya cewa ni ba d'an halak bane batare da an buk'aci hakan daga gare ni ba!!" Musty ne yayi wannan maganar cikin t'sananin bak'in ciki da kuma takaicin halayyar sa yana mai fashewa da wani irin Kuka kamar ba namiji ba! Sannan kuma ya d'aura da fad'in "tabbas dik abinda way'annan bayin Allah suka fad'a gaskiya ne babu k'arya kan rage masu salary nasu da akayi,amma kuma fa ita mamallakiyar ma'aikatar wato Zulaylha AbdulWaali bata da masaniya akan dik wannan abubuwan dake faruwa! Hasalima watanni biyu zuwa Uku da suka gabata ita da kanta tayi mawa dik wani ma'aikaci dake aiki k'arin salary na naira dubu goma goma,ni kuma ta k'aramin naira dubu ashirin amma kuma naci amanar ta na gagara yin aiki da zuciya d'aya t'sakani da Allah!"

Shiru Musty yayi,yana kallon tafin hannayen sa cike da d'acin zuciya da kuma muzanta da yasa CM gyaran murya yace, "Muna jinka ci gaba"

Saida ya jim kamin yaci gaba da shaida masu dik wasu shawarwari da suka yanke da mahaifiyar sa da irin yadda suke cin hakkin jama'a tinda dama basu san zafin naima ba saina hassada da kuma rashin godiyar Allah!!"
Kowa dake wajen jinjina kai yake kawai cike da d'imbin mamaki na wannan al'amari mai kama da ta t'suniya ko kuma suce shirin film.

Wani irin kallo Abbah ya aika ma Mamy dake ta faman share zufa akai-akai da yasa hanjin cikin ta kad'awa ba k'arami ba sabida mugun t'soron Abbahn daya dirar mata lokaci guda!!! "Abinda zaki saka man dashi kenan Aishatu? Nace abinda zaki saka man dashi kenan?"  Yayi maganar cikin t'sananin t'sawa da hargowa daya sa Mamy hant'salawa zuwa bayan C_M jikin ta d'aukar b'ari kamar mazari! Dad ne ya rik'e Abbah da k'yar tare da wasu police d'in sabida k'ok'arin da yake wajen ganin yayi nasarar jibgar Mamy!! Ummi ta jima da sanin irin k'aunar da Musty ke mata,wanda wani zubin in ta zauna ita kad'ai takanyi tunanin zata iya yin rayuwar aure dashi sabida bashi da wani aibu ko nakaso idan aka cire rashin asalin sa,wanda kuma shima idan mutum mai hankali ya auna zai gano cewa bashi da wani laifi dangane da rashin asalin nasa,tinda bawai anyi shawara dashi bane kamin a haifesa,amma kuma saidai kash! Wannan abinda ya faru yasa taji wani irin mummunar t'sanar sa ya sauk'ar mata cikin zuciya,da take jin ko dik duniya da abinda ke cikin ta zasu taru akan ta bazata tab'a yadda ta aure shi ba!

Anty Khadee kam da yaran ta sun zama y'an kallo ne kamar wasan kwaikwayo suna kallon ikon Allah! Da k'yar aka samu Abbah ya zauna mazaunin sa tana dafe kansa dake barazanar t'sagewa kamin CM ya yanke hukuncin da yake ganin shine dai-dai babu batun zuwa kotu.

Mamy da Musty zasu biya each and every ma'aikaci dake cikin wannan station d'in cikin sati guda wato kwanaki bawai,sannan kuma baza'a kulle su ba,amma fa idanuwan y'an sanda na kansu ta yadda idan ma suka aikata wani mummunar abu ta hanyar samun kud'in sun sake d'aura ma kansu laifi ne,wanda a wannan gab'ar kuwa baza suyi masu sassauci ta wani sanayya ba,yanxun ma dalilin da yasa bazasuyi masu terere ba sbd girma da kuma mutuncin da Abbah ke dashi cikin garin ne in ba haka ba tabbas abinda za'ayi masu sai ya zarce wannan d'in.

Sosai su Dad sukayi ta bama Abbah hak'uri kamin ya yadda akan bazai sallami Mamy da d'an ta ba bayan rubuta yarjejeniya akayi masu bayani  tare da tabbacin cewa dik wani abinda suka fasa both gida da kamfanin idan aka kawo kudin nasu sai an gyara idan yaso sauran a raba masu! Wanda hakan kuma yasa suka fara jin haushin kansu ba kad'an ba gashi yanzu suma da tasu asarar🤣😂.

Haka nan suka tattara suka koma gida,inda Ummi kuma suka wuce asibiti da Anty Khadee sabida yadda ita Ummin keta faman d'ingisa k'afar tata dake masifar yi mata ciwo tare da taimakon Anty khadeen,wacce dama y'an sandan ne suka taho tare da ita bayan ta farfad'o batare da an duba mata k'afar tata ba.

Tin a hanya banda bombomi da masifa babu abinda Abbah keyi,cike da takaicin Mamyn.
Da isar su gida kuwa Dad ya masu sallama ya wuce gidan sa,sabida lokacin kusan k'arfe takwas na dare ne.
Wanka Abbah yayi bayan yayi sallar la'asar,magriba da isha'i ko cin abinci bayyi ba ya fito daga gidan nasa batare da yabi ta kan su Mamy ba zuwa wani had'ad'd'en restaurant yayi masu order na abinci da su drinks da dik wasu abubuwan da ya kamata asaima mara lafiya ya wuce zuwa asibitin bayan ya kaima Aymana da Nuraaz nasu da suke ta kallon su hankali kwance,tinda su ba gama gane mai duniya ke ciki sukayi ba.

B'angaren Mamy da Musty kuwa tinda suka dawo gida...……...……✍🏽✍🏽

_GARI YAYI ZAFI😂🤣_

*vote*
*comment*
*share*
  
*OUM MUMTAZ✍🏿*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now