part 31

63 8 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...?*

*©️OUM_MUMTAZ* 

_WANNAN LITTAFIN TIN DAGA FARKON SA HAR K'ARSHEN SA NA SADAUKAR DASHI GA ~MSS FLOWER🌸🌸~ MARUBUCIYAR:_
~LAFAZI~
~AR SO~
~SARKI~
~GUMBAR DUT'SE~
_SON SO FISABILILLAH❣️💃🥰❣️❣️_                          
   
           *Chapter 31*

******** Hakan kuwa ta kasance......!

Domin kuwa bayan sati guda dayin wayar tasu Babi dake mat'sayin Uba kuma waliyyi wajen Uncle J kamar yadda YAYA BABBA ya nad'a shi da kuma Dad d'in Jiddah tare da Baban Asmy da wasu mutane guda biyu suka zo har gida naima wa Jafar auren Zulaykha...!
Wanda in tak'aice ma masu karatu,basu suka baro gidan Abbah ba saida aka t'saida ranar biki nan da 3month kamar yadda suka buk'ata!

A kuma wannan ranar Ummi tayi kuka iya kuka sabida jiyo k'amshi rabuwar ta da muradin zuciyar ta na sake kusanto ta,sai ya zamana Mamy da ta ladaftu ba kad'an ba a wajen Abbah tare da Anty Khadee da abin ya masifar yi mata suka had'u suna lallashin ta,had'i da kwantar mata da hankali gudun kamuwa da wani ciwon.

Ranar dik wanda ya kalli fuskar Abbah sai ya tabbatar da irin farin cikin da yake ciki sabida murnar auren d'iyar sa k'wallin k'wal a duniya...!
B'angaren Uncle J kuwa dik budirin wannan naiman auren nasa da yake sam sam ba'indiyar matar sa bata da labari,sabida bari yayi bazai fad'a mata ba sai nan gaba idan abin yayi sauran kadan!

A gefe guda kuwa kusan ko da wani lokaci suna lik'e da waya shida Ummi da itama k'arfi da yaji take k'ok'arin koya ma kanta soyayyar sa amma abin yaci tura!
Bayan sati guda da tambaya tare da saka rana Ammin su Yaya,mom Jiddah,Um-asmy tare da wasu matan daga cikin dangi suka kai kayan godiya kamar yadda al'ada ta tanadar,kowa kuwa sai son barka yake  sabida ganin Ummi da sukayi sosai ta kwanta masu a zuciya!

Ammi ma kuwa kamar ta goya ta a baya,sabida Allah nah gani tin ranar da ta fara d'aura idanun ta akan yarinyar sosai take masifar birge ta sabida sanyin ta da kuma rashin son hayaniya irin na d'an ta.
Inda ko ta wani b'angare guda biyu aka fad'a harkar biki gadan gadan babu kama hannun yaro,Mamy gyaran Ummi ciki da bai kasancewar ta cikakkakiyar kanuriya a ranta tana mai jin ina ma ace d'anta ne zai aure Ummin amma tasan hakan bazai tab'a faruwa ba,har duniya ta nad'e! Musty dama shikam yajima da yi ma gidan Abbah k'aura zuwa Borno sabida naimo uban sa da kuma dangin sa sabida yasan ko ba a goran ta masa a yanzu ba,to kuwa tabbas a lokacin da yazo naiman aure sai ya fuskanci gagarumin k'ask'anci.

Inda Anty Khadee kuwa Uncle J ya aiko mata da kud'in da zasu sayi lefe da dai sauran abubuwa...!
Wato a b'angaren Abbah idan kuka ga yadda yake narka uban dukiya wajen saya ma y'ar sa set na d'aki da parlo bugun zamani sai kunsha mamaki,kaya ne na kece raini fiye da tunanin mai tunani, gasu kuma masu quality bawai local ba

A lokacin saida Ummi tayi kukan rashin dangi ba kad'an ba,domin kuwa har aka shiga cikin satin biki idan kazo gidan bazaka samu wani dangi ba sai k'awayen Mamy wanda suma basu da wani yawa tare da Anty Khadee da ita kuma kan wuni acan gidan su tin auren yayan ta za'ayi...!
Takan yi Allah wadai da mahaifiyar ta,sabida gani tayi inda ace maman ta batayi abinda tayi ba,babu abinda zai sa Abbah ya bar gidan sa na haihuwa batare da tunanin komai ba!

Jiddah tare dasu Asmy sune k'irjin biki,da kuma wasu dayawa daga cikin k'awayen su da sukayi mata kara,domin ko tin satin bikin da ya kama wuni suke mata tin safe sai dare suke wat'sewa a barta da aminiyarta!

Ana gobe d'aurin aure ango ya d'ira tare da tasa tawagar ta can suka had'e dana nan Nigeria aka tafi wani babban hole da sukayi dinner a ranar,sabida ana d'aura aure ango ya masu booking na flight zasu wuce.

A wajen dinner da Ummi ta d'aura idanun ta akan Yaya da kuma Husnah wacce cikin ta ya zama babba sosai haihuwa yau ko gobe saida taji wani irin mashi ya chaki zuciyar ta mai kama da kishi,sabida ganin yadda suke ta faman tarairayar junan su! Wanda UNCLE J da ganin amaryar tasa ya kusan zautar dashi saida ya rasa gane kanta sabida yadda tafara rusan kuka baji ba gani, daga wajen dinner wuri ya rikice da hayaniyar mai ya samu amarya take irin wannan kukan,amma babu wanda yasan tak'a maimai abinda ke damunta, Haka nan dai kowa ya wat'se ana ta k'ananun maganganu kan kodai auren dole za'ayi mata take irin wannan kuka!?

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now