Part 16

79 11 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...!!*

*©️OUM_MUMTAZ✍️*
                                

           *charpter 16*

********A lokacin ne kuma gidan ya idasa b'arkewa da hayaniya,sabida akoi kawayen amarya irin y'an kaud'i na bani na iya.
Su Jiddah ne tare da Zulaykha da wasu k'awayen su na nan Abuja suka sake tarban su cike da karramawa,wanda har zuwa lokacin Husnah na nannad'e cikin lafaya sai sharar k'walla take gwanin ban tausayi,Zulaykha taso taga fuskar amaryar da tazo domin ta amma bata sami damar hakan ba,sabida shirye-shiryen tafiya dinner da yan matan suka kacame dashi,inda itama amarya aka d'auko _munash beauty_ tazo ta sake fesa mata kwalliya mai kyan gaske.

Kowacce daga cikin su kam masha Allah babu na kushewa,inda Amarya kuma kwalliyar ta, ta fita daban dana kowa sbd nata d'in special ne.

Zulaykha da Jiddah ba k'aramin kyau sukayi ba,suma sun fito fes fes abin su,cik'as d'aya shine na rashin kwalliyar da Zulaykha tayi,wanda ko kwalli bai ga fuskarta ba,sabida dama ita tin can ba mutum bace mai son shafe-shafe,natural beauty nata take a yawancin lokuta,sabida ko powder irin na y'an mata bai ganin fuskarta.

Amma kuma hakan bai sa ta zama koma baya ba cikin su,kasancewar ta jik'ak'k'iyar shuwa arab gaba da baya.

A lokacin da suka fito madaidaicin harabar t'sakar gidan sun tadda motar da za'a d'auko amarya ne kawai,inda motar da k'awaye zasu shiga suna ta waje.

Zulaykha da Jiddah kuwa,Jiddah ce tayi driving nasu a motar da ita Zulaykha tazo dashi,sun isa hole d'in kuwa cikin k'ank'anin lokacin a cikin jerin motocin aboka nan ango.

Waje kam masha Allah,domin kuwa komai yayi dai-dai (inji wani mawak'i😻),cike da nat'suwa da kuma waye wa irin ta y'an Abuja aka fara gudanar da wannan k'ayataccen dinner,tinda Zulaykha ta d'aura idanun ta akan fuskan amarya da ango a lokacin shigowar su cikin hole d'in ta naimi dik wani natsuwa,gami da courage d'in da tazo dasu sun tafi,sabida abinda idanunta suka gane mata yafi k'arfin abin da k'wak'walwarta kan iya d'auka a dai-dai wannan lokacin! Nan take idanun ta suka kad'a sukayi jazir! Dik magana gami da jijjigata da jiddah kanyi akan su shiga filin rawa amma ta gagara mot'sawa,bata sa tsawon lokacin data dauka cikin wannan mummunar yanayin ba sai ji tayi an d'auke ta kamar wata babyn robber an fice da ita daga cikin hole d'in.

Wanda kuma har an kammala k'ayataccen dinner d'in,dik Zulaykha bata cikin hayyacin ta,wanda haka yasa hankalin jiddah ya tashi ba kad'an ba,k'anin Dad d'in su jiddah dake da wajen 39-40yrs,wanda ya kama masu wannan hole d'in kenan,shine yayi jihadin d'aukar Zulaykha daga wajen bacin an gama tattaunawa,wanda kuma sam ita Zulaykha bata ma san anayi ba,sabida yadda tayi loosing na hankalin ta a wannan lokacin.

Can gidan su Ummin jiddah dake cikin tashin hankali take ma uncle d'in nata kwatan ce,a lokacin wajajen k'arfe goma tayi na dare,inda suka dannan horn,leko kai mai gadi yayi,ya gano jiddah,wanda hakan yasa bai b'ata lokaci ba ya wangale masu gate d'in,cike da natsuwa  ~uncle jafar~ yayi parking na motar tasa a parking lord.

Abbah kuwa gaba d'aya hankalin sa ya karkata ne izuwa ga ita Zulaykha d'in da har zuwa lokacin bata dawo ba,dik yabi yasa kansa a damuwa,haka nan yake ji a jinin jikin sa kamar wani abu mara dad'i ya faru da y'ar tasa,dikda yana da sanin inda take amma ya gagara zaune ya gagara t'saye tinda yaga wajen karfe tara tayi bata kira ba,bacin kuma bata dawo ba,sannan kuma tin d'azun yake k'iran layin ta amma bata dauka ba,zirga-zirga yake ta faman yi cikin parlon sa yana kai kawo,Mamy kuma na zaune can d'akin ta ko a kwalar rigarta.

Musty ne ma dai shima yabi ya damu,inda yake taya Abbah d'in jaje shima yana daga zaune akan kujera,HORN d'in motar Zulaykha da suka jine ya sasu rige-rigen fitowa da sassarfa har suna bige junan su! Daga Abbah har Musty d'in cak suka tsaya suna kwalalo idanu waje sabida ganin Zulaykha da sukayi hannun Uncle j d'in babu alamar numfashi tattare da ita,ga kuma jiddah da hannun ta ke rike da kwamut'san Ummin fuskarta na bayyana irin tashin hankalin da take ciki.

********Tasha azaba kam iya azaba a wannnan ranar,domin kuwa saida ta kwan ta sake yini kamin Allah ya t'sauwala mata wahalar ta! Banda masha Allah babu abinda Baba Rabi ke an bata a lokacin da ta gama karbar haihuwa ta Alina d'in tare da wata dattijuwa sabida 3ples din da ta santalo jazir dasu,kalar fatar uwar su.

Goya Baba Rabi ne kawai Alhaji bayyi ba a lokacin da ta ke shaida masa haihuwar matar tasa,t'sabagen farin ciki da ta cika masa zuciyar sa,take labari ya karad'e cikin babban gidan lungu da sak'o,wasu kanyi farin ciki,masu hankalin cikin su kuwa kanyi bak'in ciki k'warai da gaske,sabida sanin makomar yaran da basu ji ba,ba kuma su gani ba,kamar yadda suke gani Alhaji bai d'auki rayukan jarirai a bakin komai ba,indai akan abin duniya ne babu abinda bazai iya ba.

Yaran sai callara kuka suke gwanin tausayi tinda suka b'illo duniya,sabida rashin d'umin jikin mahaifiyar tasu da itama take ta kanta,domin kuwa baccin wahala take ta faman yi mai cike da wasu irin mafarkar marasa dad'i,sai faman had'a gumi take.

Baba Rabi dake kula da Alina sosai take matik'ar tausaya mata ba kad'an ba,tayi farin ciki da wannan haihuwa kwarai,domin kuwa kaf cikin matan Alh dake cikin gidan babu wacce ta tab'a  haifan y'an biyu ballantana akai ga har uku,saidai kuma kash!!! Idan ta tuno makomar rayuwar yaran takan ji bak'in ciki fiye da tunanin mai tunani!

Kallon yaran Alhaji yake cike da tsantsar k'aunar su a lokacin daya shigo,harma yakan ji cikin zuciyar sa anya kuwa zai iya aiwatar da k'udirin sa da yayi zaman jira na tsawon shekaru 25???

Baba rabi a zuciyar ta banda addu'a babu abinda take,kan Allah yasa kar Alhaji ya butulce ma uban giji akan kyautar yara d'ai d'ai har guda uku da yayi masa cikin lokaci guda!

Alina tasha bacci ba kad'an ba,inda still Baba Rabi ce ke kanta har ta farka,inda ta taimaka mata wajen kimt'sa jikin ta ta fito fes abinta,kallon yaran nata dake dunk'ule wuri guda suna bacci tayi fuskarta cike da tsantsar farin ciki,wanda ganin yaran nata da tayi cikin k'oshin lafiya yasa ta naimi dik wasu ciwon jikin da take tattare da su ta rasa!

Wato wani irin kauna ce fiye da kima dangane da yaran ke sukar zuciyar ta! kauna ta tsakanin y'ay'a da iyayen su,wanda har ma ya zarce hakan,ni ban ma san ta yadda zan maku baya ni ba!

Mace guda d'aya ce,sai maza guda biyu! Sosai suke samun kulawa daga ta ko wanne b'angare na cikin wannan gida har na tsawon sati guda! Inda ranar suna na zagayo wa aka rad'a masu suna _BASSAM da BAZAM_ sai kuma d'iya macen _BASMA_!

Wasu irin mutane takan gani suna shigowa kallon yaran nata da sam sam hankalin ta bai kwanta da su ba,inda dik wanda ya shigo sai ta ga yabi yaran nata d'aya bayan d'aya an shafa masu kai da sunan zuwa barka! Haka nan take jin wani irin mat'sanancin fad'uwar gaba na riskar ta a dik lokacin da taga wani bak'on fuska yazo da sunan ganin yaran nata,ga babu halin ta hana sabida gudun matsala t'sakanin ta da Alh.
Zuwa can dare da misalin karfe goma Baba rabi tare da Alina suka keb'e,tsawon awanni suka d'auka suna tattaunawa wanda ni kaida banjin abinda suke fad'a.

*vote*
*comment*
*share*
  
*OUM MUMTAZ✍🏿*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now