Part 23

64 9 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...?*

*©️OUM_MUMTAZ✍️* 

_WANNAN LITTAFIN TIN DAGA FARKON SA HAR K'ARSHEN SA NA SADAUKAR DASHI GA ~MSS FLOWER🌸🌸~ MARUBUCIYAR :_
~LAFAZI~
~AR SO~
~SARKI~
~GUMBAR DUT'SE~
_SON SO FISABILILLAH❣️💃🥰❣️❣️_                             
   

           *Charpter 23*

******** "Miyasa kika fiye rigima ne da taurin kai yanxu my dear" Yaya ya fad'a yana mai sake shigar da Husna jikin sa,gami da goga mata lafiyayyen sajen fuskarsa akan fuskarta da yasa jikin ta sakewa,tana lumshe  idanunta da suka d'an canza launi daga farare zuwa d'an jaaa.

Cikin murya can k'asa-k'asa tace "Ayya dai Yaya! Wallahi kaine gaba d'aya kabi ka chanza man tin da batun wannan cikin ya shigo,harma gani nake yanzu baka k'auna ta kamar yadda kake so na a baya,sabida sai ya zamana cewa mutum bai k'aunar ka ne,bazai so had'a jini da mutum ba,wanda kuma gashi ni yanzu hakan kake nuna man a fili baka k'aunar had'a zuri'a dani da nake kyautata zaton ka daina k'auna ta ne yanzu kamar baya."Ta idasa maganar tana mai fashewa da kuka mai matik'ar tab'a zuciya,da yasa jikin Yaya yin sanyi ba kad'an ba,tausayin ta ne ya sake samun mat'suguni cikin zuciyar sa da yasa shi sake rungumeta da kyau yana faman lallashin ta had'i da gaya mata kyawawan kalamai masu sanyaya zuciya da nan take taji damuwarta ta yaye, alamu sun nuna ya safko daga wancan akidar tasa mara tushe.

Sai da suka yi wanka suka fito abin su suna ta faman zuba k'amshi kamar babu abinda ya faru,wanda tin daga wannan ranar Yaya ya fara bata wani irin kulawa na musamman da yasa hankalin Husnah sake kwanciya.
Sosai yake tattalin ta da abinda ke cikin ta babu ji,babu gani dikda kuwa har cikin zuciyarsa wannan ra'ayin nasa na k'in son haihuwa na nan bai goge ba.

****** A k'ofar gidan sukayi parking na motar,inda suka fito hannun Jiddah rik'e da wata babbar bak'ar laida da Zuly ta kama mata gefe guda.
Waleed ne ya fito daga gidan nasu zai tafi shago sayo biscuit ya ci karo da su Jiddah d'in dake kiciniyar shigowa da laidar.

Washe baki yayi idanun sa na kan Jiddah cikin muryar sa data fara bud'ewa sabida yanzu suna cikin 15yrs shida Hamad yace, "sannun ku da zuwa Anty Jiddala kuma my daughter ta ta kaina."

"Yauwa Baffa Walidi sannu ko?" ta fad'a tana mai dire masa laidar gaban sa,b'ata fuska yayi kamar zai fashe ya kallo inda Zuly ke t'saye ta k'ura masa ido sosai tinda taga fitowar yaron da bata tab'a ganin sa ba sai yau yace "Anty mai kyau jimin wannan matar daga zuwan ta zata wani ceman Baffa kamar ta samu t'sohon Abujan can(Yaya Babba)."

D'an saita kanta Zuly tayi ta b'ata fuska had'i da hararar Jiddah d'in tace "Ki kiyayi ni fa jiddala." Itama tayi maganar cike da t'sokala da yasa suka fashe da dariya baki d'ayan su.

Sosai Waleed ya birge Zuly dikda cewa yau yau d'innan ta fara sanin sa,inda ya karb'i abin nasu ya shige dashi zuwa cikin gidan yana ci gaba da t'sokalar Jiddah tana biye sa,ita kuma Ummi sai faman murmushi take suka rufa masa baya,da sallama d'auke a bakin su suka shigo cikin gidan inda suka tarda su baki d'ayan su yaran zaune kan tabarma suna ta hirar su gwanin birgewa kowa fes-fes dashi babu k'azan ta.

Ammi dake d'aki ta juyo hayaniyar yaran ta fito daga d'akin ta da murmushi a fuskarta,har k'asa suka kai suka kwashi gaisuwa wajen AMMI dake tambayar su mutanen gida.

"Hala wannan itace Zulykha ko Jiddah?" Ammi ta tambaya tana mai k'ure fuskar ita Zulyn da kallo kamar mai son gano wani abu,wanda hakan yasa Ummi d'in dik taji ta takure tana ta faman sunkuyar da kai kamar mara gaskiya.

Murmushi Ammi tayi tace, "Ga dikkan alamu d'iyar tamu akoi kunya ba irin su Oh-oh ba kuwa" B'ata fuska Jidda tayi wai ance mata bata da kunya dik suka saka mata dariya.

"Ammah bata gida ne banji mot'sin ta ba." Hidaya ce ta ansa ma Jiddah da fad'in ta tafi unguwa ko minti goma ba'ayi ba kuwa."

"Allah ya dawo da ita lafiya" suka had'a baki wajen fad'a Ummi da Jiddah.  Da sallama Waleed ya shigo gidan yana mai rairawa wak'ar sa kan bazai samma kowa ba sabida karma su tambaye sa kan ya sammasu alamun y'an rowa yau sun kusa-kusa,dariya dik sukayi masa inda Ummi keta faman kallon sa sabida yadda yaron ke birgeta tana sakin murmushi.

Ruwa Hamad ya sayo masu mai sanyi ya kawo masu,inda Mima ta k'arasa girkin da takeyi ta zubo masu a babban tray baki d'ayan su harda Ammi.

Gaba d'aya Ummi a takure take da zaman Ammi d'in sbd sanin da tayi cewa itace mahaifiyar Zulaym Shuwa sabida t'sant'sar kamar da sukeyi da junan su ko ba a fada ba.

Sai da rana ya tardo inda suke kamin suka koma d'akin Ammi d'in da hirar tasu. Sosai suka sha fira a gidan,inda wuni ranar cur sukayi sa wanda wani irin shak'uwa ne na ban mamaki ya shiga t'sakanin Ummi da Waleed a wannan ranar,da zata tafi ma yace zai bita idan yaso sai ya kwana a wurin Anty khadee amma Ammi tace bai isa ba,ya bari idan Ammah ta dawo sai ya tambaye ta yaje ko a weekend ne,haka nan suka tafi Waleed sai faman gunguni yake an hana shi bin Anty mai kyau..

Itama Zulyn sai taji babu dad'i amma haka nan ta share kawai suka tafi bacin sun ma Ammi d'in bayanin kayan da suka kawo masu ita da AMMAH daga HAJJA.

Saida ta ajiye Jiddah a gida kamin ta wuce nasu gidan ana k'iran magriba suka had'u da Abbah tare da Musty zasu wuce masallaci.
Flat na Mamy ta wuce da sallama a bakin ta,bata tarda ta a parlo ba,don haka sai ta wuce d'akin ta,wanka ta fara yi kamin ta d'auro alwala ta gabatar da sallar magriba,ba ta mot'sa a wurin ba,saida tayi sallar isha'i kamin ta shirya kanta cikin sleeping dress nata ta fito zuwa parlon su data tarda Mamy,Abbah,Musty,Aymana,Nuraaz da Anty Khadee zaune kan dining har sun fara dinner.

Da shike tasan tayi laifi sai taki zuwa gefen Abbah tayi zaman ta daga can kujerar da ba kowa kasancewar yanzu dining d'in mai d'aukar kujeru goma sha biyu ne,don haka akoi enough wajaje.

Kowa cin abincin sa yake,amma banda ita dake ta faman wasa da yat'sun hannun ta kanta a k'asa alamun bata da niyyar cin abincin,daga lokaci zuwa lokaci takan sakin murmushi ita kad'ai idan ta tuno da rigimar da Waleed ya tada mata d'azu kaman wani k'aramin yaro.

Sai da Anty khadee da Musty suka tambaye ta bazata ci abinci bane? Ta daga masu kai batare data bude baki ba tana kallon Abbah ta wut'siyar ido sabida ganin yadda yayi kicin kicin da fuska kaman bai ganta ba kwata-kwata. Dik dan akan takai magriba a waje bacin kuma yace karta dad'e.

Sumi-sumi ta wuce d'akin ta bayan ta masu sallama kan zata kwanta,Anty Khadee ma ta wuce nata flat din tare da yayan ta,Musty ma ya wuce aka bar Mamy da Abba tinda dama yau girkin na Mamy ne,shiysa akayi dinner a part nata kamar yadda Abba ta t'sara masu baki daya.

Mamy ma bata b'ata lokaci ba ta wuce d'akinta aka bar Abbah shi kad'ai zaune kan kujera yana kallon news,nan kuwa ba kallon bane ya dauke masa hankali,sai tunanin rashin cin abinci da Ummi din tayi yana t'soron kar ulser ta kamata.

Da kansa ya had'a mata shayi mai kauri daya sha madara da milo ya wuce zuwa dakin nata,zaune ya tadda ta kan gadonta cikin shirin bacci da wayarta a hannun ta tana kallon pics din da sukayi a gidan su Waleed dazu.

Bakin gadon nata ya zauna cikin sassauta fuskar tasa da tin dazu take a hade yace, "Oya karbi ki shanye ki bani cup dina Ummi na"

Babu musu kuwa ta ansa tana sha a hankali-hankali, inda gefe guda kuwa hankalin ta na kan wayarta,wajen kallon wani pics da sukayi gaba ki dayan su harda Ammi din suna dariya.

*vote*
*comment*
*share*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Hikayelerin yaşadığı yer. Şimdi keşfedin