Part 22

94 11 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...?*  

*©️OUM_MUMTAZ✍️* 
                        
   

           *Charpter 22*

******** Sun shiga rud'u iya rud'u gami da tashin hankali,domin kuwa mutuwar Kaka ba k'aramin girgiza mazaunan unguwar yayi ba,kasancewar sa mutum ne shi mai sauk'in hali da sanin yakamata,tare da taimakon na k'asa dashi,dikda cewa ba wai k'arfi ne dashi ba,amma dai yana k'ok'artawa dai-dai gwargwadon iko,Aisata da MUSTY ma ba k'aramin tashin hankali suka shiga ba daya zarta na kowa.

A ranar da ya rasu aka mik'asa gidan sa na gaskiya,Waali ma ba kad'an yayi kukan rasuwar Kaka ba a wannan ranar sabida yadda ya zaunar masa mat;sayin mahaifi akan lamuransa na yau da gobe tin sauk'ar sa cikin garin KANO.

Ummi kuwa na wajen Aisata da mutuwar mahaifin nata ya girgiza ta ba k'arami ba,inda Musty ma sosai yaci kukan sa sabida yadda ya fara wayo a lokacin yasan cewa dik wanda y mutu bazai tab'a dawowa ba.

Saida akayi kwana bakwai da rasuwar Kaka kamin aka daina zaman k'ofar gidan kowa ya wat'se sabida dama mutanen da akayi zaman tare ne bawai dangi na jini ba.

Tin daga wannan lokacin sai ya zamana dik wasu larurorin Aisata da d'anta Musty Waali ya d'aukar masu,domin kuwa yanxu sun zamto kamar wa da k'anwa ne,ga kuma Ummi dake sake girma abinta kyawunta t'sant'sa na sake fitowa kamar y'ar turawa.

Manyan unguwa ne suka had'u akan Waali wajen basa shawarar auran Aisata sabida yanayin kusancin dake t'sakanin su,zuciya bata da k'ashi,ba fata ake ba,shaid'an kan iya k'awata masu junan su koda a gaba ne,gwanda su tari abin tin daga yanxu.

Ba don Waali na da niyyar sake aure a rayuwar sa ba,sai don gujema abinda manyan suka hango masu yasa shi amincewa da auren Aisata d'in,ko ba komai ta wannan hanyar zai iya saka ma MARIGAYI da taimakon sa da yayi a baya.

An d'aura auren Aisata da Waali wanda kuma UMMI da MUSTY kan k'ira su da MAMY,ABBA. A lokacin da Ummi ta kai 4yrs ne kuma arzikin Abba ke dad'a bunk'asa babu ji babu gani,kasuwanci yaci uban na da da,domin kuwa har daga wani gari yakan saro takalman sa ya maida shagon nasa babban BOUTIQUE da ake ji dashi cikin kasuwar.

Sannan kuma ya zuba yaran da zasu na kular masa dashi,Mamy da d'an ta ma sunyi b'ul-b'ul dasu abinsu gwanin sha'awa sbd yadda Abbah bai rage su da komai ba na jin dad'in rayuwa.

Soyayyar dake t'sakanin Abba da Ummi kuwa saima abinda yaci gaba ba wai baya ba,Abba yasa su a islamiya ita da Musty wanda zuwa lokacin sun tashi daga wannan unguwar sun koma RIJIYAr zaki a wani gidan su mai d'an girma amma ba har can ba.

Sannan kuma yasa su a makaranta ta private mai kyau da suke tafiya tin safe basu dawowa sai yamma,Akoi wani abokin Abba da suka had'u a yawon kasuwan ci mai suna _YUSUF_ wanda shi kuma mazaunin garin Abuja ne tare da matar sa,da kuma y'arsa guda d'aya mai suna JIDDAH. Sannan kuma iyayen sa mazaunan Abuja d'inne amma asalin su y'an garin KADUNA ne.

Daga abokan taka na kasuwanci aka koma aminta mai lasisi,wanda kuma cikin k'ank'anin lokaci Waali yayi wani irin kud'i harma ya zarta abokin sa Yusuf d'in (Dad na Jiddah kenan).

Wanda hakan yasa Dad yima Abba kwad'ayin zaman cikin Abuja dik da yadda take da t'sadar rayuwa,Abbahl kuwa bai musa ba,inda ya sayi wani babban filin sa acan cikin garin Abujan unguwar Maitama ya dank'ara uban ginin sa na gani na fad'a kamin ya kwashi iyalan sa bayan ya d'aura way'anda ya yarda dasu akan kasuwancin nasa.

Komawar sa cikin garin Abuja kuwa Mamy da MOM matar Dad suka zamto k'awaye dik da ba wani har can ba,sannan kuma Ummi da Jiddah ma haka nan,sai Musty da shi kuwa kan t'saya masu a harkar karatun su mat'sayin sa na yayan su.

Abba da kuma Dad ne suka had'a hannun jari su biyun su suka bud'e wani babban kamfanin su na saida takalma na fata a cikin garin ABUJA mai suna _~Z and H NIGERIA LIMITED~_ .

Sun kuwa bud'e wannan campany d'in da k'afar dama,domin kuwa cikin Abinda bai gaza shekaru biyar ba,sunayen su ya shige da fice a k'asashen k'etare bama Nigeria kad'ai ba,kud'i yaci uban nada,wanda hakan ya fara saka Mamy fara jin takaici kan miyasa Abbahl d'in bai saka Musty a mat'sayin magajin sa ba sai UMMI(kuji min kokari)

Yara suna girma suna sake yin wayo,wanda tin Ummi na k'arama MUSTY yake son ta tin bata kai haka ba,ya riga su kammala secondry school inda Abba ya kaisa k'asar china yayo k'aratu a fannin business kamar yadda shima yayi,kuma yake da burin y'ar sa ma ta gado sa.

A lokacin da suka kammala sec sch dik wani abu da ake kira da budurci ya gama bayyana tattare da su baki daya,inda kuma Dad d'in Jiddah ne ya nema masu admission a BUK kano suna karanta course d'aya business sabida a commercial class dama suka zauna sec sch nasu.

Kud'in Alina da Waali ke d'an jujjuya mata daga lokaci zuwa lokaci ya fara gina ma Ummi wani madaidaicin kamfani shima na sarrafa takalma ne kamar nasu,amma bai kai shi girma ba.

Dawowar su hutu na farko ne ta fara fuskantar hali na i don care daga Mamy d'in ba kamar da,da take ji da ita ba. Wanda ita kuma sam bata san mainene silar haka din ba.

Lokacin da Musty ya dawo sai suke tafiya wajen aiki tare da Abba wanda kuma Mamy bata so haka d'in ba,taso ace shima Abba ya bud'e masa campany kamar yadda taga yana yi na UMMI.

Musty kuwa hakan sam-sam bai wani dame sa ba,lokacin da suka kammala degree nasu fannin business suna da 22yrs,inda Abbah zai tafi k'asar India domin kafa wata kamfanin su shida Dad d'in acan da ak'alla zai d'au t'sawon shekara guda,tare da Mamy Abbah ya tafi,da kuma JIDDA da UMMI d'in sabida suyi masters nasu a fannin business d'in na t'sawon shekara guda daya tal.

Watan su shida acan Abba da Mamy suka dawo,sannan Dad da Mom na JIDDA suma sukaje suka idasa watanni shida din kamin suka tarkato tare da su UMMI d'in da suka kammala karatun su suka dawo gida.

A lokacin ne kuma Abba ya d'anka ma ZULAYKHA (UMMI) ragamar kula da kamfanin ta daya bud'e mata da dukiyar mahaifiyarta,wanda hakan kuma ya sa Musty saka rai shima za'a bashi nasa amma yaji shuru,hakan ya sosa masa rai amma sai bai nuna damuwar sa ba,inda ya buk'aci da a had'a shi waje guda da ita Ummi sabida bazai so ace wasu mazan na kalle masa ita ba,har Abbah yace zai bashi manajer na campanyn amma yace sam shi saidai ya zauna a mat'sayin P A nata ta yadda zasu rink'a kasancewa tare a ko wani lokaci.
Sosai Mamy taji haushin hakan kuwa,ta ringa masa masifa kamar zata cinye sa d'anye amma shikam ko a jikin sa.

Jiddah kuwa mahaifin ta bashshi da ra'ayin barin ta yin aiki har sai tayi aure idan mijin ta ya aminta sai ya d'aura ta akan nasa kasuwan cin zuwa gaba,dan hakan ita kusan koda yaushe tana gida ne abinta daga gidan kakan nin ta da kuma y'an uwan su babu inda take zuwa.

Musty da Ummi tare suke dawowa daga wajen aiki wasu lokutan,wajen zuwa kuwa kullum tare suke fita da Abba ya ajiye ta a nata shi kuma ya wuce nasu wajen.

Batun arxikin sa da ya baro acan KANO ma ba'a magana sabida yadda arziki keta faman shigo masa ko ta ina babu ji babu gani sai dai ya d'aga hannu yace Alhamdulillah.

Musty ba k'aramin birge JIDDAH yake yi ba,amma kuma bata bari kowa yasan hakan ba,sabida ganin yadda yake masifar son aminiyar ta tin suna k'ananu.

Mamy kuwa kullum cikin fad'a ma Musty take kan bazata barsa ya auri ZULAYKHA ba amma bai yadda ba koma saurararta bayayi tinda yaji shid'in menene asalin sa.
Abbah ma kuwa tin gama war su Zulaykha makaranta ya bata tarihin rayuwarta kaf a lokacin da ta buk'aci hakan babu abinda ya rage mata. Tayi kuka iya kuka a lokacin da taji halin wacce ta t'suguna ra haife ta,amma hakan baisa ta t'sane ta ba,sabida mahaifiya ta wuce gaban wasa koman lalaci.

Mat'salar kud'i kuwa da ake dannewa ma'aikata hakkin su ba aikin kowa bane saina Mamy da Musty,wanda a bayyane kuwa hakan Aikin Abba ne da Zulaykha dayasa kullum cikin t'sine masu ake,wanda kai t'saye zan iya kiran hakan da suna *RIJIYA TA BA DA RUWA*
_guga ya hana_  inji hausawa.

Ma'ana kuwa.........🖊️

*vote*
*comment*
*share*
  

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now