Part 14

75 8 0
                                    

*RIJIYA TA BADA RUWA...!!*

*©️OUM MUMTAZ✍️*
                                 

           *charpter 14*

******** Sauk'owa take daga matakalar jirgin sama daya sauka a cikin filin babban jirgi wato international airport dake garin Abuja! Wanda ya kwaso su daga kasar Dubai, sanye take cikin wata doguwar riga ta abaya mai kalar shud'i irin sararin samaniya,watoh sky blue! Wanda akayi ma gaban rigar ado duwatsu mai kyan gaske!
Ta yane kanta da babu kitso da siririn mayafin daya kasance mahad'in rigar ce! Farar fuskarta kuwa shimfide take da zallar farin cikin dawowarta kasarta ta gado wato Nigeria,wanda tayi tafiya zuwa kasar dubai a makwannni biyu da suka gabata,wajen yin sayayyan kayayyakin ta na ado da kwalliya.

Hannun ta kuwa rik'e yake da wani madaidaicin akwati maicin kaya kala uku! Inda idanuta suka sauka akan mahaifinta dake ta faman rarraba idanuwa sabida son gano ta inda yar lelen nasa zata b'ullo! Domin kuwa ba karamin kewarta yayi ba sanadin wannan tafiyar,da tinda suke bata yin tafiya ta kwana wani wuri ba tare dashi ba,wanda ko shine zayyi tafiya zuwa wani gari ko kuma kasa to k'afarta k'afarsa ne,domin ko bai yadda yaje wata uwa duniya ba,ba tare da d'iyar tasa ba!
Jin irin kyakkyawar rungumar da aka basa ne,ya shaida masa yar lelen sa ya iso! Sosai Abbah ya nuna murnar sa ta dawowar Zulaykha tin a filin jirgi kamin su idasa zuwa can ainahin gida!

Inda acan ma kuwa Zulaykha ta samu tarba na musamman,wanda ta tabbatar ba aikin kowa bane,saina mahaifinta! Sai nan-nan da ita Musty yake yi kamar zai maida ta cikin sa,dik kuwa da irin uwar hararan da yake ganin Mamy na aiko masa amma haka nan yayi mirsisi abinsa kamar bai san tanayi ba!

Tayi wanka,taci abinci gami da fiddo ma kowa tsarabar data kawo masa,inda na Abbahn ta yafi na kowa!
Wanda hakan kuma ya sosa ma Mamy rai,wai Zulaykha bata dauke ta mahimmanci ba,kamar yadda ta dauki mahaifinta(kujimin k'ok'ari fa☹️ a gun matar nan).

Washe gari.

Zulaykha ce zaune tsakiyar kan luntsumemiyar katifarta,ta tankwashe kafafunta! hannunta rike da waya tana karanta wani littafi mai suna ~RAYUWAR DARAKHSHAAN~ wanda wannan marubuciyar data saba kashe ku da dadadan littafan ta irin su :
_nuna so gaban kishiya._
_zatoh._
_ayshat._
_ta'ummu ka(aure saida kaka)._
_nigeria ko niger(wacece bora)._
_hamdeeyerh._
_nuraaz(treasure of noor)._
_silar al-majiranci._
_Aymana (romantic story_
_kunji munafuki_
tazo tayi _rayuwar darakhshaan_!
ina a halin yanxu take kawo maku daddadan labarinta mai taken ~RIJIYA TA BADA RUWA~ ba kowa bace wannan marubuciyar wayannan face littafan "OUM MUMTAZ"😉

Sosai littafin ke taba mata zuciya sabida ganin irin wofantar da shaan da iyayenta keyi! Wanda kuma hakan yasa ta tuno tata mahaifiyar!

K'iran daya shigo wayar dake hannun ta ne,yasa ta dakatawa daga karatun da take,hadi da sakin karamin murmushi sabida ganin wacce ke k'iranta!
Kamin ya yanke tayi recieving,had'i da manna wayar tata a kunnen ta tace, "Amincin Allah ya tabbata a gareki aminiyar arziki,fatan kina lafiya?!"

Daga ta can bangaren Jiddah dake gidan kakan ninta tace, "Tare dake my k'awalli! Fatan kin dawo lafiya??"

"Lafiya kalau wallahi! Ya kuma gajiyar zirga-zirga?" Zulaykha ta tambaya sabida auren Uncle na Jiddah d'in da akeyi! wanda bata samu damar halarta ba,sabida tafiyar da tayi!

"Zirga-zirga kam munata fama ai! Yanzu haka ma an daura auren ne! muna jira su dawo daga can inda aka d'aura auren sabida hada gagarumar dinner din da zamuyi anan abuja din,dafatan kema zaki zo ko?"

D'an murmushi ta daura akan fuskarta,dikda yadda yau ta tashi cikin tsananin faduwar gaba da bata san dalili ba tace, "Anya kuwa zan iya fidowa Jiddah? nida wai yau da nake son na huce gajiya amma kike son fito dani ba tare dana shirya ba?"

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now