part 34

84 10 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...!*

*©️OUM_MUMTAZ*

      
*34*

A wani irin mugun tashin hankali daya zarta tunanin mai tunani Yaya da dama kwata kwata bai cikin hayyacin sa ya saki yarinyar dake hannun sa tana callara kuka ya kaima wannan nurse d'in wani irin mugun naushi inda Allah ya taimaka da mugun azama Dad ya fisgeta tayi k'asa wanda hakan yasa shi kaima jikin ginin da suke t'saye naushi da nan take hannun sa ya fara bleeding,cikin wani irin hanzari Anty Khadee da itama tana wajen ta taro jaririyar datake ta faman tsala ihu baji babu gani sabida gigitar da kwakwalwarta yayi!

Wani irin azababben mari Ammih ta wat'sa ma Yaya da bai gama dawowa cikin nat'suwat shi ba cikin t'sananin t'sawa da takaicin sa ta fara zuwa masa masifa babu ji babu gani akan gangancin da yake so yayi da rayuwar k'aramar yarinyar da yau yau aka kawo ta duniyar! Wanda shi kuwa Yaya baima san tana yi ba sabida suman tsayen da yayi tin lokacin data mare sa,inda kwakwalwarsa keta faman son yin aiki daya kamata amma ya gaza yin hakan!

Kafafun sa da suka masifar yi masa tsami ya fata jansu kamar wanda aka watsama ruwan kankara zuwa dakin da yake da kyautata zatohn zai samu ASMA'Un sa! Ai kuwa sosai zuciyarsa ta buga wani irin tsalle sabida ganin mutanen da suka zo asibiti tare dasu nata faman share kwalla sun saka wata dake kwance kan katifar fuskarta lullube cikin wani shudin bedshet ko fuskar ba'a gani!

A lokacin tunani ya farayi,wanda idan zuciyar sa na aiki dai dai,ya kuma daura maganar da wannan likitar ta masu dazu kenan wannan gawar ta Ma'un sa ce...!?

Wani irin kuzari ne ya saukar masa lokaci guda da yasa shi isa zuwa gadon dasu Mom suka saka gaba suna famar hawaye,hannayen sa na masifar rawa ya yaye wannan lullubin da akayi,wani irin murmushi ne ya subuce masa sabida ganin fuskar Husnah dake fidda wani irin annuri fuskarta da murmushi kamar a kira sunan ta,ta ansa.

Bata fuska yayi sosai sannan ya kalli mutanen dake masa kallon tausayi ya ce, "So wai dik wannan kuka na mainene? Ni dama nasan waccan shegiyar likitan k'arya take da zatace man Ma'u na na rasu,bayan kuma munyi ma junan mu alkawarin kasancewa tare da junan mu har abada."

Kowa dake wajen zuba masa ido yayi ganin da sukayi alamun ya zauce ne idan ba haka ba yana kallon gawa kwance a gaban sa yana karyatawa...?

Shigowar su Dad da wasu likitocin ne ya hargitsa ma Yaya kwakwalwa yana masu borin kar katon daya kuskura ya taba masa matar sa amma basu bi ta kansa ba sabida already an riga da an gama dik wasu cike cike a halin yanzu ma ambulance aka kawo zasu tafi da ita gida!

Ai kuwa sai gani sukayi Yaya ya zube warwas a k'asa babu alamun numfashi tattare dashi a lokacin da yakuma tabbatar da cewa Ma'un sa is no more. Baban Asmy kawai aka bari asibitin kan da zarar ya farka sai suma su biyo su gidan Yaya Babba sabida can zasu wuce a halin yanzu, ai kuwa tin kamin su k'arasa labarin ya iske gidan da nan take kuwa ya barke da wani irin koke koke babu kakkautawa,Ammah da itama tana gidan kuwa ta gagara gaskata abinda ake fadi na rasuwar diyar tata sai a lokacin da aka shigo da ita da yasa su Waleed tare da sauran yaran dake gidan fara kuka cikin tsananin tashin hankali sbd ganin gawar Anty Husnah!

Cikin kankanin lokaci kuwa saiga gidan YAYA BABBA ya cika makil da mutane dikda kasancewar goshin magriba ce a lokacin! Wani irin kuka Ammah keyi mai matik'ar taba zuciya a lokacin da tasa gawar diyar tata a gaban ta da sai uwa ce kawai kan iya fahimtar wannan yanayi da Ammah ke ciki idan akace diyar ki ko danki sun ansa kiran ubangiji...!

Ammih kuwa ba kankame da jaririyar itama tana sharar kwalla na rashin Husnan da kuma maraicin da wannan jaririya zata fuskanta,ga kuma halin da suka baro yaran ta na kila wa kala a asibiti.

Sai da Yaya babba dasu Babi suka shigo har cikin gida suka tsawatar masu kamin suka bar wannan kururuwar suka kama karatun qur'ani mai girma!

Hajja da wata tsohuwa data kasance yar uwar su da kuma Ammah da itama tayi tawakkali ta mika lamuran ta ga Allah ne ta samu dangana suka hadu sukayi ma Husnah wanka a wannan daren inda aka kintsa ta,aka barta zatayi kwanan keso!

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now