part 33

71 12 0
                                    


*RIJIYA TA BA DA RUWA...!*

*©️OUM_MUMTAZ*

*33*

Cike da t'sananin bacin rai bayan kowa ya zauna an nat'su Yaya babba ya kalli side d'in da Rushni ke jingine cikin harshen hausa tinda dama ta koyi hausan ya ce,"Amma dai a gaskiya kin matik'ar bani kunya yau d'innan Rushni! Kishi hauka ne? Ko kuma akanki aka fara yin kishiya da zaki je ki zubda man da mutuncin gida na wajen taron jama'a...? gaskiya baki kyauta mana ba,sannan kuma baki kyauta ma kanki ba akan haka d'in da kikayi gashi dik kinbi kin jima kanki rauni,yanzu idan t'saut'sayi ya gifka kika halaka kanki mai zaki je kice ma ubangijin ki a mat'sayin ki na musulma?"

Share hawayen dake zubowa cikin idanun ta tayi,cikin muryar dake nuni da cewa tana jin jiki tace, "PAPA wallahi ba laifi ba bane,laifin J ne da bai fad'a man zai k'ara aure ba tintini sai kawai jiya da daddare wata cousine sister nah ta k'irani daga INDIA tana tambaya ta wai dama mijina zai k'ara aure shine ban fad'ama family na ba? Wanda hakan ya sani tambayar ta dalilin ta na fad'ar hakan,inda ta turo man wano short vedeo din da akayi sa wajen dinner da har ya zaga duniya. Hakan ne yasa naji raina ya b'aci sosai inda nayi booking na jirgi a daren jiyan sabida inzo naji dalilin sa b'oye man kan zai k'ara aure,cikin sa'a kuwa na samu wanda zai tashi k'arfe Uku na dare wanda ban d'auko komai nawa ba sai fad'a ma wani Uncle d'ina dake nan Nigeria yana aiki a airport d'in kan ya naima man mota gani nan zuwa,inda jirgin mu na s'auk'a na bincike adress na gidan su yarinyar da zai aura tinda naji a yau ne za'a d'aura auren ba'a riga an d'aura ba,tare da taimakon Map dana saita akan motar nazo gidan har mai afkuwa na afku. Amma ina naiman afuwar ku akan abinda na aikata nayi nadama insha Allahu makamancin hakan bazata sake faruwa ba."
Ta k'arashe maganar tana mai fashewa da kuka sosai sabida azabar dake ziyartar kwanyarta akan lahanin da tayi ma kanta...!

Ai kuwa take kowa dake wurin ya fara k'ananun maganganu yana baima Jafar daya sunkuyar da kansa laifin mafarin faruwar komai ba...!

"Ai kuwa Allah shi k'ara gwanda ma da kika mashi hakan wallahi,ai wallahi koni akayi wa hakan sai inda k'arfi na ya k'are,don kawai sabida zalinci zai wani maki kishiya batare da sanin ki ba? Ai kuwa in dai nice akayi wa hakan abinda aka maki abinda zanyi sai ya zarta naki...!" Ai kuwa gwab'e ma Husnah baki Ammah tayi cike da t'sananin kunya da kuma tashin hankali sabida jin zantukan da yarinyar tata keyi cikin fusata sabida maganar da take directly daga cikin zuciyarta ke fitowa sabida mantawa da tayi a inda take kasancewarta mace mai zafin kishi.

Kowa dake wajen sosai ke kallon Husnah data tak'ark'are tana zuwa zance hatta ga Yaya da zuciyarsa ke bugawa  kan kalamana da tace inda itace sai tayi abinda ya zarta wanda Rushni tayi!! Ganin irin kallon da kowa ke mata ga kuma bangajar da Ammah ta kawo ma bakin ta tagane irin katob'arar da tayi,wanda hakan yasa taji wani mat'sanancin kunya ya rufeta sosai ba kad'an ba...!

"Tashi kizo kusa dani Mamana." Yaya babba ya fad'a yana mai yafito iya Husnar da hannun sa,ai kuwa babu musu ta mik'e da k'yar zuwa inda yake sabida nauyin da cikin nata keyi ta samu waje ta zauna,tana kuma lura da irin kallon da mutanen wajen ke binta dashi data rasa gane na mainene...!

Cikin sigar dabara Yaya babba ya kama hannun ta ya ce, "yanzu kina nufin yau idan takwara ya k'ara aure batare da sanin ki ba kema abinda zaki aikata sai ya zarce wanda y'ar uwarki Roshni tayi uwata?" Cike da jin kunyar mutanen dake wajen ta rufe fuskarta da tafin hannun ta tinda dama Yaya babba sun maida shi ne kaman kakan su tace, "Nasan ma Yaya bazai tab'a man haka ba."  "So idan kuma yau akace Mahaifin ku Babi ya aura masa wata yarinyar batare da sanin ki da kuma takwara na ba laifin wa zaki gani anan? Kuma shin zaki iya illata kanki!" A wannan lokacin sosai taji gaban ta ya fad'i,wanda hakan yasa ta samu nat'suwa k'irjin ta na bugawa tace, "Nasan Babi yana k'aunata tabbas bazai tab'a had'ani da abinda zai iya cutar dani ba sabida shid'in garkuwa ne gare ni tare da mahaifiyata da kuma k'anina...!"

Murmushi sosai dik y'an cikin parlon sukayi sabida jin dad'in kalamanta inda Yaya yaci gaba da fad'in, "To ina so kiyiwa maganar da zan fad'a maki kyakkyawar fahimta,ki gane cewa komai na duniya dake faruwa Rubutaccen Al'amari ne da ubangiji ya riga daya gaba t'sara kayan sa tin kamin asan za'a halicci wani halitta...! Don haka ina so ki kwantar da hankali,ki kuma fahimci dik bayanin da zan maki ki dube sa da kyakkyawar fahimta ba wai don bama sonki bane hakan ya faru saidon dama hakan Tin ran gini tin ran zane ne...!"
Haka nan taji k'irjin ta na mat'sanancin bugawa sabida k'wak'walwarta data fara hasaso mata abinda ake shirin fad'a mata da d'azun taji ana ta gulmar amma bada bama zancen nasu mahimmanci ba...!

Tiryan-tiryan Yaya babba yayi mata bayani ta yadda zata fahimta batare da t'sikewar zuciya ba har k'arshe! Kowa dake wurin zuba ido yayi sabida aga irin reaction d'in da zatayi inda ita kuma tayi k'asa da kanta dikda yadda takejin numfashin ta na k'ok'arin fin k'arfin ta ta bud'i baki da niyyar yin magana amma saita gagara,wanda hakan yasa Yaya ya rufe taron bayan doguwar nasihar da yayi masu tare da umartar Hajjo ta kula da yanayin ita Husna d'in sabida gudun faruwar mat'sala.

A tak'aice ranar Husnah kwana tayi cikin mawuyacin hali da bata bar kowa ya fuskanci halin da take ciki ba sai mahaifiyarta wato Ammah da tayi ma y'ar tata farin sani ciki da bai...! Inda itama saida suka kebe a daren ta sake kwantar mata da hankali sosai,inda Ammih ma ta d'aura da nata kowa dai nata fadin albarkacin bakin sa amma ita bata cema kowa k'ala ba,saida ta bisu da ido...!

Yaya kuwa tin rabuwar su a parlon YAYA bata sake sashi cikin idanun ta ba har zuwa lokacin,dikda yanayi na rashin dadi da Jafar ke ciki,hakan bai sa shi taya d'an uwan nasa murna tare da fatan alkhairi ba,ya karbi kaddarar sa a yadda tazo masa tinda Allah bai nufa cewa Zulaylka matar sa bace!

Tin a daren ranar yayi masu Booking na jirgi washe gari da sassafe suka d'aga daga Nigeria tamu ta gado,zuwa k'asar Australia...!

Acan b'angaren gidan Abbah kuwa labarin daurin auren daya fasu da asalin ango zuwa kan dan uwan sa ya riga daya gama karade dik wani lungu da sako,masu gulma nayi masu jaje nayi kowa dai na tofa albarkaci bakin sa...!
Suna da niyyar maida kaya Dad ya shaida masu ba sai sun dawo dashi ba,shi Jafar d'in ya barma d'an uwan sa komai da komai mat'sayin gudummawa,wanda hakan yasa Zuly jin tausayin J d'in dikda bata son sa...! Da shike dama bawai dangi bane sai dik aka wat'se a ranar gida ya zamana shiru kamar ba gidan biki ba,sai Asmy da Jidda tare da wata k'awar su ne kawai ke nan gidan tare da Ummin,Mamy kuwa sosai ta kasa ta t'sare ta hana Ummi fita daga d'akin ta,su Jidda ma don dole suke nan !

Asmy a daren itama ta tafi gida tare da Umaima k'awar tasu kenan aka bar Jiddah dake mat'sayin babbar k'awa ita kad'ai...! Anty Khadee kuwa ita da Jiddah sosai suke nan nan da Ummi kamar t'soka daya a miya!

Acan gidan YAYA kuwa washe garin ranar Husnah ta tashi da mat'sanancin nakuda tin cikin dare amma abu yaki ci yaki cinye wa sabida edd nata bai cika ba,kawai tashin hankali ne da yayi mata yawa ya tasar mata da nakudar babu shiri,idan kuka ga yadda Yaya ya birkice masu kan shi sai ya saki Zulaykha a ranar sai kusha mamaki,fadi yake ai dik ta sanadiyyar auren ta da aka lika masa batare da anji ra bakin sa bane ke neman illata lafiyar matar sa!! A ranar saida YAYA ya nuna masa bacin ransa sosai kamin ya sarara masu aka kwashi Husnah dake matik'ar galabaice zuwa asibiti...! Inda tasha Allurai da dik abubuwan da suka dace ayima nai nak'uda amma shuru kake ji kamar an shuka dusa...! An wuni ana abu d'aya hankulansu dik a matik'ar tashe yake gidan baki daya,sai aka kawo ma Yaya takadda yasa hannu za'a shiga mata C S sbd zata iya gamuwa da yoyon fitsari idan basu dau mataki ba! Haka nan yana kuka da komai yayi signing cikin k'ank'anin lokaci  aka kammala komai aka shiga da ita therter room...!

T'sawon awa daya da rabi wata nurse ta fito daga ciki hannun ta nannade da baby girl dake ta faman callara kuka kamar ana yankan nama jikin ta...! Gaba daya mutanen dake wurin suka fara hamdala ana rige rigen karbar yarinyar fuskokin su na washewa cikin tsananin farin,inda Ammah kuwa sai faman leka bayan nurse d'in take ko zataga fitowar diyar tata amma wayam...!

"Ya jikin matata kuma?" Yaya dake k'ank'ame da yarinyar kamar za'a kwace masa ita ya tambaya...! sunkuyar da kai NURSE d'in tayi cikin muryar rauni tace "am sorry to say......maman baby ta ansa k'iran ubangiji😭😭😭😭😭"

*vote*
*comment*
*share*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now