Part 21

73 9 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...?*  

   *©️OUM_MUMTAZ✍️*                      
   

           *Charpter 21*

******** Tin daga wannan ranar a hankali rayuwar Waali tare da y'ar sa ya fara gangarawa cikin garin Kano ta dabo tumbin giwa,inda kuma shak'uwa gami da zumun ci na sake k'ulluwa t'sakanin su da gidan Kaka Baban Aisata,inda yaji asalin su ashe suma y'an asalin garin Maiduguri ne KANURI,inda zama ne ya kawo su nan garin Kano d'in sabida guje ma t'segumi na mutane akan iftila'i na cikin gaba da fatiha d'in da Aisata tayi ya fad'a masu.
Wanda hakan yayi sanadiyyar rasuwar mahaifiyar ta,inda suka tattaro yana su yana su suka dawo nan d'in bacin ta haihu,wanda ba kowa bane wannan yaro illah Mastaa.
Ummi kuwa sosai take samun wadatacciyar kulawa daga Aisata,Masta,Kaka da kuma uwa Uba mahaifin ta,wanda hakan yasa cikin k'ank'anin lokaci tayi wani irin girma na ban mamaki ga kuma k'oshin lafiya.

Babu wanda ta sani sama da mahaifin ta dik da irin kulawar dasu Aisata ke bata amma ko bata sake masu kamar yadda take sakewa da mahaifin ta, a gefen kasuwan ci na saida kayan trader da Waali keyi kam sai dai ya d'aga hannu yace "Allah na gode maka!"
Bashi da wani mat'sala daga shi har y'arsa sai na kewar ahalin sa daya t'sallako ya baro mahallin su a can jihar Borno!  A kullum dare da kuma waye wa ta duniya t'sanar Alina da mai hali irin nata na dad'a bunk'asa ne cikin zuciyar sa,wanda yake jin ko duniya da abinda ke cikin ta zasu k'are wannan t'sanar da yayi mata bazai tab'a gogewa ba!

A lokacin da Ummi ta cika 1yr da sunan "Abbah na" bakin ta ya fara bud'ewa cikin gwaran ci kamar yadda a kullum ta duniya Waali ke sata a gaba yana koya mata ambatar wannan sunan da Allah ya sa ta fara anbatar hakan kuma cikin ikon sa.
"Mamy" sunan da take kiran Aisata kamar yadda Mastapha ke kiran ta.

A fannin kasuwan cin Waali kuwa sai abin da yaci gaba,inda yazo ya koma cikin babbbar kasuwar dake cikin Kano bacin ya bud'e babban shagon sa da yake saran takalma daga manyan shaguna yana sayar wa bacin ya d'aura ribar sa kamar yadda sukeyi da iyayen sa tin acan Borno kamin k'addara ya kawo sa nan garin d'in.
Kuma sosai yake samun ci gaba,wanda kuma Aisata ce ke kulawa da ita Ummi d'in babu t'sangwama balle kuma hantara,wanda hakan yasa yarinyar bata da damuwa ko kad'an,kayan wasa iri-iri kuwa babu wanda Abbah nata bai saya mata.
Yau sun tashi ne da tashin hankali na rasuwar Kaka bacin gajeruwar jinyar da yayi na t'sawon kwana uku.

******** "Yaya ga can lunch naka fa na kammala ko na kawo maka nan ne,naga kamar baka son mot'sawa daga inda kake???"  Husnah ce ke wannan maganar a lokacin da take t'saye daga bakin kitchen tana fuskantar Yaya dake kwance kan kujera 3seater yana lat'sar wayar sa,jikin sa sanye yake da wani 3quater sai kuma riga armless,wanda hakan yasa murd'ad'd'en surar jikin sa ta cikakkun maza sake bayyana matik'a.

Batare da ya d'ago ya kalle ta ba,ya girgiza mata kai alamun bai jin yunwa,nannauyar ajiyar zuciya ta sauke cike da rashin jin dad'in halin rashin damuwa da yake nuna mata ta tako zuwa cikin parlon,inda tayi ma kanta gurbi a kan k'irjin sa kamar zata shige jikin sa bacin ta lumshe idanun ta tana shak'ar daddad'an k'amshin turaren sa da taba gajiya da shak'a tinda ta samun wannan cikin.

Ba tare da ya mata magana ba ya sake gyara mata kwanciyata a jikin sa ta yadda zata fi sakewa ya ci gaba da danne-dannen sa,wanda hakan ya sata sake shigewa jikin sa sosai kamar mage tana sakin ajiyar zuciya.

Abinda take masa ne yasa shi sauk'e wayar tasa a gefe guda,inda lek'o k'ansa ta inda fuskarta yake,waro idanu yayi cike da damuwa a fuskar sa sabida ganin kuka fa ashe take yace "lafiyar ki kuwa dear!?"
kamar dama jira take ta fashe da kuka sosai,wanda hakan ya sa shi mik'ewa da ita suka idasa shige bedroom d'in dake mat'sayin mallakin ta.

******** "Mamy da Abbah na tafi gidan su Jiddah wai zan rakata gidan y'an uwan su sai na dawo!" Ummi ce ke wannan maganar a lokacin da take zaune kan kujerar da Abban nata yake ta jinginar da kanta a kafad'ar sa.

D'an bubbuga bayan ta Abbah yayi yace "toh a dawo lafiya Mamana,amma fa karki dad'e sosai kina jina ko??"

"Insha Allah Abbah na!" ta fad'a a lokacin da take mik'ewa,"Mamy sai na da wo." ta fad'a a lokacin da take ficewa daga flat d'in nasu zuwa na Anty khadeeja,zaune ta tadda ta a parlo da kuma su Nuraaz da Aymana suna kallo .
Suna cikin gaisawa suka ji sallama Jiddah,wanda hakan yasa basu wani b'ata lokaci ba nan d'in suka fice bacin sun ma Anty Deeje sallama,a motar Jiddah yau suka fita,inda suka kama hanyar Suleja kamar zasu tashi sama.

******** A mugun t'sorace yake,amma hakan bai sa shi fasa fitowa daga cikin motar tasa ba jikin sa na karkarwa,sai da ya tabbatar da cewa dik guje-gujen da ake akan hanya an d'an ragu,kamin ya waiga gefe da gefe ya tabbatar babu wanda hankalin sa ke kansa,dikda a d'an t'sorace yake,hakan bai sa shi dakatawa daga tinkarar gaban motar tasa ba,zuciyar sa take tayi mummunar bugawa sabida kallon mace da yayi t'sirara haihuwar uwar ta kwance shame shame jini na zuba akan goshin ta,ta inda glass d'in gaban motar tasa ta fasa mata.

Wata zuciya na ce masa yayi cilli da ita cikin sauran gawarwakin da ke zube akan hanyar ya gudu kamin y'an sanda su zo,inda wata zuciyar kuma ta kwab'e shi da hakan da bai san dalili ba,kamar wanda ake tunkud'a shi ake basa umarni ya bud'e boot na motar sa da akoi wani troley nasa da kuma wani babban bargo ya ciro bargon,saida ya nannad'e ta cikin bargon kamin ya saka ta cikin boot d'in bacin ya maida kayan sa dake ciki gefe yana ta faman waige-waige kaman mara gaskiya,da wani irin mugun gudu shima ya bar wajen sabida jin jiniya na y'an sanda da suka samu labarin abinda ke faruwa.

Kan kwaltar shall dik wasu motoci kowa ya fece abinsa,sai motocin police keta faman kai kawo tare da likitoci da aka kawo ambulance daga kaduna,inda aka kwashi gawarwakin mutanen dake wajen aka wuce asibiti da su,ma'aikatan kuwa sai faman al'ajabi suke sabida ganin manya-manyan y'an siyasa na k'asar tamu da aka san da zaman su,d'ai-d'ai ku ne sabbin fuska,cikin k'ank'anin lokaci labarin abubuwan dake faruwa ya cika states na 9ja kan asirin wasu masu mulkin ta tonu,wanda mutane da dama kan masu tofin ala t'sine,an k'ira iyalan ko wanne daga cikin bayan an gama dik abubuwan da ya kamata aka basu gawarwakin suka tafi dashi.

Nan da nan kuwa aka mance ma da shafi kansu a rayiwa sabida dama basu ajiye wani abu mai kyau da in an gani za'a ringa tunawa da su ba,balle kuma ayi masu addu'a.

(Sun zo a banza zasu koma a banza😭Allah ka cire mana kwad'ayi da kuma son abin duniya da zai kai mu ga aikata aikin da nasani ranar gobe k'iyama🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻🤲🏻😭😭😭😭).

Sosai yake sharara uban gudu akan titin da ya sada shi da cikin garin Kaduna babu b'ata lokaci,unguwar Gomna road ne dama inda zaije wajen mahaifiyar sa domin kai mata ziyara daga can Abuja d'in,kasancewar yau ranar friday ne.

Ya jima zaune cikin motar yana ta faman sauk'e numfarfashin gajiya kamin ya samu da k'yar ya fito daga cikin motar tasa yana sharar zufar da ta jik'e masa jikin sa ba kad'an ba.

Sallama ma da k'yar ya samu damar yin sa a kan fatar bakin sa,inda ya tadda mahaifiyar sa zaune kan sallaya akan baranta t'sohuwa tukuf da ita tana ta faman jan charbi.

Zubewa yayi a gaban ta yana mai jin wani irin zazzafar hawaye na zuba daga cikin idanun sa da bai san na minene ba?

"Lafiyar ka kuwa HIMU?? Wani abu mummuna ya faru ne akan d'aya daga cikin ku kake irin wannan kukan?"

Da k'yar ya samu damar t'saida kuka nasa kamin ya shaida mata dik abubuwan daya faru akan hanya har kawo tahowa da yayi da macen da baida sanin cewa mutum ce ko aljan? Rayayya ce ko kuma matacciya...??

_SO MASU KARATU DAGA NAN LABARIN ~ALINA~ ZAI D'AN DASA AYA,ZAN SHIGA LABARIN WANNAN MATASHIN DA AKA KIRASA DA HIMU,DOMIN JIN CIKAKKEN TARIHIN SA IDAN YASO IDAN AKAZO DAI DAI WANNAN GAB'AR DA MUKA T'SAYA LABARIN ITA ALINA D'IN DA KUMA NASA ZASU TAFI AKAN GAB'A GUDA INSHA ALLAH🥰🥰🥰💃_

*vote*
*comment*
*share*
  

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now