part 30

59 9 1
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...?*

*©️OUM_MUMTAZ* 

_WANNAN LITTAFIN TIN DAGA FARKON SA HAR K'ARSHEN SA NA SADAUKAR DASHI GA ~MSS FLOWER🌸🌸~ MARUBUCIYAR:_
~LAFAZI~
~AR SO~
~SARKI~
~GUMBAR DUT'SE~
_SON SO FISABILILLAH❣️💃🥰❣️❣️_                          
   
           *Chapter 30*

******** WAshe gari da misalin k'arfe goma na safe,Yaya ya ajiye Husnah,Waleed da Hamad k'ofar gidan Abbah kan idan ya taso daga wajen aiki shima zai shigo su gaisa.
Idan kuka fuskar Waleed kamar gonar auduga sabida yadda yake ta faman d'auki na ganin Anty mai kyau,d'aya daga cikin sabbin ma'aikatan da aka kawo ce bayan ta kaima mai gadi abinci daga part na Anty Khadee ta masu jagora!!

Da sallama suka kut'sa kansu cikin parlon,Husna ce a gaba sai Hamad tare da Waleed da suka take mata baya!
"Sannun ku da zuwa k'annen arziki yanxu kuke tafe?" Anty Khadee ta fad'a cike da t'sant'sar farin ciki a lokacin da ta fito daga kitchen sabida jiyo mot'sin su!

"Ai kuwa dai mune da zuwan safiyar nan an sako mu a gaba Anty" Dariya dik suka shek'e dashi Anty Khadee tace, "Babu wani sako ku a gaba da akayi,kuka san ko zamuyi y'ar gida ne da Anty mai kyau d'in da ake ta faman ambata? Ai jiya da dare munyi waya dasu Babi sun kuma shaida man na t'sammaci zuwan Alhaji mai gida yau"

Nan dai suka sake gaggaisa sosai,Aymana,Nuraaz da Ummi ne suka fito daga kitchen da in kuka gansu sai kun rik'e baki sbd yadda sukayi butu-butu da fulawa!

"Bak'i mukayi ne Anty? Sannun ku da zuwa fatan kunzo lafiya?" Ummi ta ce ma Husnah da itama kanta saida ta yaba da kyawun halitta irin na Ummi d'in,abinda ya farkar da ita shine muryar mahaifiyar ta da ta jiyo tattare da Ummin babu banbanci ko na sisin kobo!

"Lafiya klaou Anty mai kyau" ta ba ta ansa tana k'wak'ulo murmushin yak'e sbd yadda take jin gaban ta na t'sananin bugawa!

"My man's kunzo lafiya ko??" Ai kuwa mat'sowa Waleed yayi yace, "suwal muka zo Anty nah,tin jiya naso a kawo ni amma mijin waccan t'sohuwar ya kasa ya t'sare!"

Da mamaki kuwa UMMI tana dariya tace "wanene kuma mijin t'sohuwa ni Zuly?"

"Wai fa Yaya yake nufi?" Hamad ya bata ansa shima yana sakin dariya,wanda hakan yasa Husnah d'aure fuska tace, "kamar a kunnen sa yau d'innan!!" wanda ma tin kamin ta gama rufe bakin ta suka bi suka rikice sunaa bata hak'uri kan karta fad'a masa su shiga tara!!

Sosai kuwa suka sha hirar su,wanda tin Husna da Ummi na baya baya da junan su cikin k'ank'anin lokaci suka saki jiki suna zuba charpter kamar dama sun jima da sanin junan su,inda suka shiga kitchen suka k'arasa girkin ma tare tana ta t'sokalar ta da maman unborn!

Bayan sallar azahar sun gama cin abincin su Ummi ta kwashi Hamad dasu Waleed tare da Aymana da kuma Nuraaz zuwa wajen shak'atawa domin su sha iska!

Husnah taso binsu sabida yadda take jin dad'in kasancewar su tare amma Anty Khadee tace "bata isa ba" sabida sanin halin Yaya bazai ga laifin Husna ba sai nata.
Sun sha yawo bana wasa ba kuwa,basu suka dawo gida bai sai bayan sallar la'asar wajajen k'arfe biyar na yamma!

Inda suka tarda sabuwar motar yaya fake cikin harabar gidan nasu,da yasa Waleed dafe k'irji had'i da fad'in, "Shikenan kuma! Yanzu nasan yau kam harara saimun ture!" Nuraaz da bai cika yawan magana ba cikin sanyin murya yace, "Hala har yanxu bai canza halin sa na t'sare mutane ba?"
"Ai abin ne ma yana girma yana sake yin linkaya in fad'a maka!!" Aymana da Ummi kuwa dariya suka shek'e dashi,dik da yadda k'irjin Ummi ke masifar bugawa bana wasa ba!

Da sallama suka shigo parlon,inda saida Ummi takai ga dafe k'irjin ta batare da kowa ya lura ba,sabida ganin Yaya da tayi a yau ido da ido sai da wani irin mik'i da soyayyar sa ya sake samun mat'suguni cikin zuciyarta tare da zazzafan kishi sabida ganin yadda Husnah ta masa rashe-rashe tana zuba masa shagwab'a shi kuma sai biye ta yake,ga kuma Anty Khadee zaune gefe sai t'siya take masu.

Mik'ar da Husnah Yaya yayi yana gyara mata zaman gyale kanta,batare da ya ansa gaisuwar dasu Hamad ke masa ba yace, "Sai ku wuce mu tafi a yawo!"  "Ka bar su su huta mana sarkin azarbabi sai ku tafi idan anyi sallar magriba!"

Ai kuwa harara ya dalla ma Anty Khadeen da yasa Ummi cikin sanyin murya da tin d'azu tayi ma kanta mazauni kan kujera tace, "ina wuni?" Kallon inda aka gaida sa yayi a karkace da yasa k'irjin sa bugawa cikin basarwa yace, "lafiya" daga nan yaja bakin sa ya t'suke ya kad'a kan su baki d'aya suka fito,inda sukayi clashing da Abba wajen da sukayi parking shima ya dawo tare da masu t'saron shi!

D'an risinawa sukayi suka gaida shi ya ansa masu cikin sakin fuska tare da tambayar su mutanen gida,wanda sai a lokacin Yaya ya tabbatar da abinda ke masa yawo tin farkon had'uwar sa Abbah kamar yasan wani mai kama dashi,sai yanxu da ya gan Waleed jere da Abbah d'in yasan inda yake masa kallon sani! Sai kawai ya basar bai bama hakan mahimmanci ba!

Abbah kuwa harda bama su Waleed money sabida yadda yaron ya masifar birge shi ba kad'an ba,ya kuma jii k'aunar sa har cikin zuciyar su! A lokacin da idanun sa suka sauk'a kan fuskar Husnah sosai gaban sa ya fad'i,sbd ganin wani irin mugun kamar marigayiya Iyami shimfid'e kan fuskar ta! Wanda kuma zuciyar sa ta fara zarga masa wani abun,amma sai kawai ya share tinda dama ance ai kowa yana da masu kamannin sa guda bakwai a duniya !

Choculate dasu ice cream d'in da suka sayo Ummi ta bama su Hamad bayan ta raga ma su Aymana nasu! Inda suka rabu cike da t'sant;sar kewa,suna gama ficewa daga cikin gidan suka kama hanyar suleja sabida mayar dasu Waleed d'in gida kamar yadda sukayi ma su Ammah alk;wari!
Basu suka dawo cikin gidan nasu ba sai wajajen k'arfe tara na dare!

B'angaren Ummi kuwa komai yinsa take cikin k'arfin hali har sukayi dinner,inda tin bayan da tayi shirin kwanciya tabi lafiyar katifar ta banda kuka babu abinda take,sabida ganin wani irin soyayyar Husnah cikin idanun Yaya ta tabbatar zayyi wuya ta samu koda gurbi guda ne cikin zuciyar sa!

Washe gari misalin 10:00am.

Ringing d'in da wayar ta keyi da naiman agaji ne ya farkar da ita daga baccin da bata samu damar yi daren jiya ba,sakamakon kwana da tayi tunani da kuma kukan son ma so wani...!
A kasalance ta zuro da hannun ta na hagu zuwa inda take da tabbacin ta ajiye wayar tata batare data bud'e idanun ta ba,ballanta kuma tasan wanda ya k'irata,tayi recieving!

Muryar wanda ta jiyo ne daga cikin wayan yasa ta d'an yamut'sa fuska ta kuma gyara kwanciyar sannan ta bud'i baki da k'yar tace, "Mun tashi lafiya uncle??"

Daga ta can b'angaren Uncle J dake k'asar Australia yace, "lafiya kalai preety na,yasu Abbah da kuma sauran mutanen gida...?"

"Dik lafiyan su,ya aiki?" 

"Alhmdlh my dear!"

Daga nan dai suka t'sunduma cikin firar tasu gadan-gadan,wanda yawanci ma shine ke magana,sai dai ta ansa masa da eh ko Ah ah...! Sannan kuma yawancin hirar tasu da suke na magiya ne kan ta basa damar turo da iyayen sa a naima mashi auren ta amma take gara masa kai sabida sanin da tayi cewa a zuciyar ta akoi wanda take so,amma kuma idan ta zauna tayi dogon nazari tana ganin kamar hakan bazai haifar mata da d'a mai ido ba,da ace ta nacema mutumin da babu d'igon soyayyar ta a zuciyar sa ita kuma tana son sa,gwanda ta bama wanda ke k'aunarta dama dikda bata son sa,tasan with time komai zai zama tarihi ne kamar ba'ayi ba!!

Gashi wanda a baya take ganin zata iya bashi damar auran ta ko da kuwa ace bata k'aunar sa ya b'ata rawan sa da t'salle(musty kenan) .So don haka kawai sai tayi deciding ta kuma bama Uncle J dama tinda taga kaf cikin maneman ta shine matured one dikda a cikin burikan ta babu t'sari na auren mai mata,and kuma datayi sake reshe kama ganye kam gwanda tasan inda dare yayi mata.

Inda a wannan ranar saita Ummi ta kuma tabbatar ma da Uncle J damar ya turo magabatan sa sabida ita ma ba dut'se bace,tafiya ake shekarun ta na sake jaa gwanda kawai tayi ma kanta fatan Alkhairi ba wai bin muradin zuciyar ta ba...!

Hakan kuwa ta kasance.........🧕🏼

*vote*
*comment*
*share*
  
*OUM MUMTAZ✍🏿*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now