Part 20

78 11 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...!!*

*©️OUM_MUMTAZ✍️*
    
                              

           *charpter 20*

******** An d'aura auren Abbah da Anty khadeeja daya samu halartar mutane da dama,dikda ba auren fari bane,inda akayi gagarumin tashin hankali da Mamy ba kad'an ba,sai da Abbah yayi mata baraza da dat'se igiyoyin auren dake t'sakanin su kamin ta shafa masa lafiya!

Su Zulaykha ma ba kad'an taji farin cikin wannan auren ba,wanda kuma ba komai ne ya jawo hakan ba,illah Allah-Allah da take kan Allah yasa  haifa ma Abban ta wasu yaran da zai na kallon su a mat'sayin nasa dangin ba wai ita kad'ai ba da idan yau ta Allah ta kasance akan ta tasan babu wanda mahaifin nata kan iya yin tutiya da shi a mat'sayin nasa.

Flat na Anty khadeeja ma daban ne,kamar Mamy,sannan kuma Abbah ya buk'aci da tazo da yaran ta idan har dangin mahaifin su sun yarda shi yayi alk'awarin zai rik'esu t'sakanin da Allah tamkar yaran sa daya haifa.

Anty Deeja na da saukin kai ba kad'an ba itama,wanda hakan yasa tasu tazo d'aya da Zulaykha,wanda kusan kullum tana can part d'in suna hirar su sabida rashin tazarar shekaru masu yawa dake t'sakanin su,wanda hakan ko sosai yake sake tafarfasa ma Mamy zuciya fiye da tunanin mai karatu!

Har zuwa wannan lokacin Zulaykha bawai ta manta da batun Yaya bane sam!! Hasali ma ranaku d'ai-d'ai ne bata zama yin tunanin sa na musamman,tinda ta san dangantakar dake t'sakanin su da jiddah aminiyarta,bacin wannan ma tana da labarin irin son da yake ma matar tasa uwa t'soka d'ai a miya!

_UNCLE J_ kam bata ma san ina ya samu number wayar ta,wanda suke d'an tab'a chart dashi dik da shashshare sa da take kasancewar sa mai mata harda d'an su guda d'aya!

Wanda ita kuma sam sam a t'sarin ta ma bata son ta auri mai mata! Ta gwammaci idan ma za'ayi mata kishiyar ita ta fara shiga gidan,idan yaso ko uku ne ma ya auro daga baya bai dame ta ba,kamar ita ace taje ta tadda su,wanda hakan yasa take baya baya da uncle j d'in,tin da ta fuskanci manufar sa amma sam baiji,saima k'ara lik'e mata da yake kamar chewing gum,dik da kuma kasancewar sa mazaunin k'asar Australia da su sukayi believing da zama da mace guda har k'arshen rayuwar su.

A lokuta da dama idan taje kwanciya bata da abin yi sai kallon pic na Zulaym Shuwa! Wanda kuma shi a nasa b'angaren sam sam bai san da zaman wata halitta mai kama da tata ba a duniya!

Wata ran takan yi kuka to her own satisfaction kamin ta share hawayen ta,wanda hakan kesa ta kwana da ciwon kai mai t'sananin gaske,amma kuma koda wasa babu wanda ta tab'a bama wani k'ofa da zai fuskanci halin da take ciki,hatta ga mahaifin ta da bata had'a sa da kowa ba a duniyar ta.

Bangaren Mamy da kuma Oga musty kam duniya ce ta sake bud'e masu sabuwa a fannin zubin adashen da suke babu k'ak'k'auta wa,inda kuma Allah ya isa gami da tsinuwa a kullum Abbah da Zulaykha sai sun sha ta yafi cikin kwando amma sam su basu da labari.

******** "Kiyi addu'a y'ata! Kiyi addu'a,domin kuwa ita addu'a makamin mumini ce! Ina ji a jinin jiki na akoi guntun rayuwar da zakiyi mai t'sawon gaske a gaba! Kije ki naimi yafiyar d'an uwan ki da kuma y'arki! Kar ki bari way'annan azzaluman suci nasara akan mu! Ki tashi kije!! Ki tashi kije nace!!!!"

Iyami ce ke wannan maganar cikin t'sananin galabaita da kuma zabar zuk'ar ruwan nonon ta da wannan halitta keyi dake mat'sayin Alhaji tin iya k'arfin sa,wanda tin ruwan nona na zuwa har saida ya fara zuk'ar ainahin jinin jikin ta ta wannan hanyar,wanda kuma wannan maganar da tayi shima dik cikin iko ne na uban giji!

"Ku d'aure man ita!!!!" Alhaji yayi maganar cike da t'sananin t'sawa da sai da d'akin da suke ya girgiza!! Amma kuma aka rasa mai tinkarar inda Alina take sabida karanto addu'ar da take ta faman yi tana kallon mahaifiyar ta amma ta gagara mot'sawa daga inda take.

Tas Alhaji ya gama zuk'ar jinin Iyami ta wannan hanya jikin ta ya saki alamun rai yayi halin sa! The same thing na abinda yayi ma iyami haka nan yayi ma Baba Rabi dik akan idanun Alina da ta zama butum-butumi tinda aka kashe mata mahaifiyar ta akan idanun ta!

Kamar wanda aka hankad'a sai gata tayi wani irin sukuwa gaban Alh daya d'akko wani abu mai t'sinin gaske bacin an mik'o masa jinjirar ta guda wato Basma dake ta faman callara kuka!

Amma kuma saidai cilli d'aya Alh yayi mata da k'afar sa sai gata can mak'ure jikin bango idanun ta ya kafe akan Alh da kuma yar tata dake ta faman cilla uban kuka gwanin tausayi.

Babu d'igon tausayi ballantana kuma imani haka nan tana ji tana gani aka k'wak'ule ma y'arta idanuwa akan idanunta,aka farke mata ciki! Aka ciro kayan cikin ta aka kuma wurgar da gangar jikin ta inda ya sakeyi ma sauran yaran nata irin abinda yayi ma wannan jinjirar agaban idanun ta ya kuma zauna ya cinye abubuwan nan t'saf yana lasar baki!

Wato fa akace wai shima kuka rahma ce ga d'an Adam! wanda Alina ta yarda da hakan tabbas a wannan ranar! Fit ta naimi da tayi kuka amma ta rasa wai ko zataji saukin rad'ad'in da take jin cikin zuciyarta ya ragu.

Wani irin shegiyar dariya ALH ya kece da ita,inda d'akin ke ansa kuwa tare da muryoyin way'anda ke tare dashi suma suna taya sa cike da t'sant'sar kafirta kamar ba jinsin su ake wulak'antawa haka nan ba dik dan sabida kwad'ayi da kuma son abin duniya!!!

"Daga yau! Daga kan jinin ki da zan shayar da kaina! Suna na zayyi fice cikin duniyar mu da jinnu da dik inda aka ambaci sunana sai an girgiza sabida k'arfin ikon da naki jinin dana ahalin ki zai k'ara man akan dikkan lamura nah zuwa kan dangi nah da dik wanda ke kewaye dani!!!"

Alh yayi maganar cike da dariyar keta,wanda hakan yasa Alina ta samu damar raba jikin ta daga jikin ginin da Alh ya manna ta bayan ta karanto addu'ar "SUB HANAKA INNI KUNTU MINAZZALUMIN!!" wanda take ta faman maimatawa cikin zuciyarta har ta fito fili! Take kuwa d'akin da dik wani abinda ke cikin ta suka fara k'arar rakin fashewa sabida komai daya danganci wannan gidan t'sagwaron t'safi ne.

"Ki dakata! Ki dakata da wannan abinda kikeyi!!"

Alh keta faman ambata sabida yadda shi karan kansa fatar jikin sa ta fara sullubewa yana zama ruwa iya zuba a wajen!!"

Suratul jinni kawai Alina data fara dawowa cikin hayyacin ta ta cafko tin iya k'arfin muryarta da Allah ya bata tana sakin rikitaccen kuka bacin ta tamke idanun ta gagam!

Ta d'au t'sawon lokaci tana karanta wannan surar da komai na cikin gidan keta faman babbakewa yana ci da wuta,tin tana iya jin ihun bil'adama dake cikin wannan d'akin cikin fitar hayyaci har takai ta kawo taji anyi wani irin wulli da ita cike da t'sananin hasala,wanda ba kowa bane mai wannan aikin face Alh dake cikin mummunar yanayi sabida yadda ayar Allah ta narkar masa da sassan jikin sa da baza su sake amfanar sa da komai ba!

A dai-dai time d'in da yayi cilli da ita gidan ya kama da wani irin tafasashshen wuta mai t'sananin azabar gaske ko ta ina! Amma kuma dikda haka dik mutanen da suke wucewa takan wannan hanyar babu abinda suke gani,kasancewar gidan yana daga kan hanya ne!

Motoci ne matafiya dake wucewa ta kan hanyar suka fara guje-guje suna bama motar su wuta sabida ganin yadda aka wat'sa abu cikin t'sararin samaniya,bacin ya kai k'asa kuma sai suga mutane ne! Tashin hankali ne sosai ya barke akan hanyar dake t'sakanin Abuja da Kaduna.

Wata motace da tazo wucewa ta wajen dake tafiya cike da t'sant'sar nat'suwa dikda guje-gujen da mutanen kan hanyar keyi,matashin saurayi ne da ak'alla zai bama 30yrs baya daya zo saitin dai-dai wajen kawai kamar ba d'an adam ba sai ganin mutum yayi ta fad'o a kan glass na gaban motar sa.

wanda hakan ya sa shi cin wani irin wawan birki a mugun razane.

*vote*
*comment*
*share*
  
*OUM MUMTAZ✍🏿*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now