Part 37

216 18 1
                                    

*OUM_MUMTAZ*

*RIJIYA TA BA DA RUWA...!*

_Finally daga wannan page din na kawo karshen littafin nan wato RIJIYA TA BA DA RUWA(guga ya hana) abinda na rubuta dai dai ina rokon ubangiji ya bani ladar shi,wanda kuma nayi kuskure wanda na sani dama wanda ban sani ba ina rokon ubangiji ya yafe man🙏🏼🙏🏼sannan kuma dik wanda na bata ma rai tin a lokacin dana fara rubuta littafinnan har kawo yau dana kawo karshen sa shima a yafe man don Allah, ubangiji ya yafe mana baki daya ameen ya hayyu ya qayyum😍😘😘🥰🥰🙏🏼🙏🏼_

      
*37*

Kamar a cikin mafarki take jin dan surutu kasa-kasa a kanta,ga kuma yadda take jin wani dan zafi zafi na ratsata da yasa ta bude idanunta tar ta sauke su akan wata matashiyar mata dake sanye da fararen kaya alamun likita ce,sai kuma ta maida idanun nata ta sake budesu but still dai wannan matar ta gani da yasata yamutsa fuska ta dafe goshin ta dake barazanar tsagewa murya can kasa kasa tace "wacece ke...?"  sister Rk da Zulaym ya kira ne har gida tazo duba ta takai duban ta ga fuskar Ummin dake matikar kumbure cike da tausayawa tace "Masha Allah sannan baiwar Allah kin farka ma ashe..."  "Uhum" kawai tace mata batare data bude baki ba,sabida yadda kwakwalwarta ta shiga tariyo mata irin cin zarafin da Yaya yayi mata.
A wannan ranar dai sosai Yaya ya afka cikin wani irin nadamar da bai taba yi ba,inda akama Ummi dinki sakamakon... da akayi da ita ta hanyar d bata kamata ba.

Dik wannan budirin da ake kuwa Ummi ta gagara sanin takamaimai hanyar da ta dace ta daura abinda Yaya yayi mata,a lokuta da dama idan ta dago kanta tana kama shi iya satar kallon ta da sai itama ta tsinci kanta da zuba masa idanun ta sbd yadda fuskar sa take babu wanda zai taba tunanin wannan fuskar zata iya aikata abinda yayi a daren jiya...

Haka nan kwanaki suka dan fara gangarawa babu abinda ya chanza tsakanin zaman su,shi a nasa wajen yana kokarin wajen ganin ya wanke bakin pentin daya lafta ma kansa a wajen ta amma sam sam taki basa fuska ballantana ma ya samu kwarin gwiwar tinkarar ta da batun bada hakuri,sabida tabbacin da take dashi wannan abinda Zulaym yayi mata ko wayanda ake ma fyade albarka kenan.

A haka nan tana shan magungunan ta,tana kuma shiga ruwan zafi kamar yadda sister Rk ta bata shawara har ta warke tsaf abinta kamar wacce batayi wani abu wai shi ciwo ba,kuma a cikin wayannan kwanakin tana iya bakin kokarin ta wajen ganin komai ya dai daita tsakanin ta da mahaifiyarta.

Abinda yayi mata dadi sosai bai wuce lokacin da ta cika wata guda ba dasu Jidda suka kawo mata ziyarar bazata kamar yadda suka saba yi mata idan zasu zo basu fadi mata sai kuwa gashi sunzo mata da labari mai dadi dangane da saka date na ranar bikinta da akayi da Musty wanda ya samo dangin mahaifin sa da suma wasu family ne manya masu hannu da shuni dake maiduguri,kuma har zuwa lokacin mahaifin sa nan nan da ransa! Gashi kuma Asmy ma nata saurayin ya fito wanda hakan yasa aka hade auren nasu rana guda.

Nan suka shantake suka sha hirar su har zuwa yamma da Yaya ya dawo,wanda sosai ya fada shima wannan lokutan sabida stress da yayi masa yawa ba kadan ba... ga kuma soyayyar Ummin da tayi masa mugun kamu cikin zuciyarsa amma yana shakkar tinkarar ta da wani batu na soyayya Sabida yasan ya cutar da ita, zai yi wuya ta aminta da cewa yana sonta.
Ummi kuwa dik wani abinda tasan duty nata ne a cikin gidan tana iya kokarinta wajen ganin ta sauke su,kama daga kan girki da tattare gida da dai dik abubuwan da suka kamata amma banda zama wuri guda tare da shi.

_Bayan wata biyu_

Zuwa wannan lokacin anyi wata uku kenan da tarewar Ummi,kuma har zuwa wannan lokacin babu abinda ke shiga tsakanin su sai gani sai hange daga nesa...lolz..

Amma fa kuwa sosai Zulaym ya mugun shan jiki ba kadan ba,ga kuma yadda yake jin wani irin azababben feeling nata na kama shi a dik lokacin da yayi arba da ita sbd yadda take masifar tsukewa da sha gayu dare da rana kamar ma wani abin da gayya takeyi...

You've reached the end of published parts.

⏰ Last updated: Aug 15, 2023 ⏰

Add this story to your Library to get notified about new parts!

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now