part 32

67 8 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...!*

*©️OUM_MUMTAZ*

*Chapter 32*

Wani irin buga t'salle k'irjin Zulaym yayi kamar ya faso k'irjin ya fad'o k'asa,a mugun razane yayi ma Babi daya d'auke kai kamar bai ga yanayin da yaron nasa ya shiga ba da kallo!! Ganin yadda jikin Zulaym ya d'auki mugun rawa ne yasa Dad rik'o hannun sa yana girgiza masa kai alamun kar yayi wani abinda ba shine ba!!!!

Cike da t'sananin tension Abbah da bai so ayi hakan ba ya kallli Abbah daya bama Babi auren Zulaykha,sannan kuma ya kalli mawuyacin halin da Yaya ke ciki,ga kuma Babi da yak'i kallon shashin da Yaya d'in yake suna gaisawa da mutane tare da masu fatan Alkhairi akan wannan auren da akayi na bazat!!

A ransa kuwa ji yake wani irin girma tare da kima da kuma darajar ahalin Babi ya rufesa lokaci guda,sabida t'samo dashi daga tafkin k'unyar da Jafar yaso jefa sa da yayi,dikda yasan fin k'arfin shi Jafar d'in matar tasa tayi.

Sallama Dad yayi ma Abbah kan bari yaje anjima zai dawo idan komai yayi settling,inda yake rik'e da hannun Yaya dake cikin mawuyacin halin ba kad'an ba! Idan kuka ga yadda idanun sa suka kad'a sukayi jazur sai kusha mamaki...!!
Baban Asmy ne keyin driving,sannan kuma Dad tare da Yaya suna baya inda ya d'aura kansa bisa k'afad'ar Dad yana jin yawun bakin sa na k'ok'arin kafewa sabida ganin wannan aure da aka lak'aba masa mai kama da almara.

Gidan Yaya Babba dake cike da taf da mata y'an biki kama daga kan su Ammah,Ammih,Um-asmh ,Mom,Anty Khadee da dai sauran su suka shiga bayan sun sa Yaya dake ta faman tangad'i t'sakanin su,suna rirrik'e shi.

Kowa tambaya yake da guntuwar gulmar sa kan lafiya?? Amma ko kallo basu isha su ba,suka wuce parlon Yaya da suka same sa sanye cikin manyan kaya yasha binjimar sa yana jan charbi tare da wani abokin sa da shima sosai girma ya kama sa suna b'allan goro!

Sosai tausayin Yaya ya kama YAYA Babba ya soma lallashin sa had'i da basa baki tare da nuna masa mahimmancin karb'ar k'addara da kuma biyayya ga za6in iyaye !
Sannan kuma yake tofe sa addu'oi da yasa nan take yaji wani irin nat'suwar da ya rasa ta na wucin gani na ziyartar ko wane lungu da sak'o na sassan jikin sa.

Y'an cikin gida mata kuwa sunyi cirko-cirko kowa na son sanin abinda ya faru,sabida ganin su Dad da sukayi d'azun sun tabbatar da cewa ba lafiya ba! Ai kuwa suna nan suna k'ananun maganganun nasu saiga Waleed tare dasu Hamad,Nuraaz da sauran bataliyar su sun shigo gidan sabida dawowa da ake ta faman yi daga d'aurin aure! Waleed da bakin sa sam bashi da sakata ne ya tak'ark'are baki had'i da zubo ma matan gidan Abinda ya faru wajen d'aurin aure tiryan-tiryan batare da ragi ko na sisin kwabo ba...!

Wani irin salati da sallallami gidan ya rud'e dashi sabida jin wannan bayani mai kama da wasan kwai kwayon daya afku cikin gidan...!! Babi da wasu mutane suka shiga wajen YAYA babba had'i da masa bayani inda ya nuna hakan ba damuwar komai bane tinda jihadi sukayo Allah bazai barsu haka nan ba! Wanda kuma a lokacin sosai ransa yayi wani irin b'aci akan abinda surukar tasa tayi dikda dama yasan aikata hakan kad'anne daga cikin halayen india da basu san wai wata abu kishiya ba.

Aikuwa cikin k'ank'anin lokaci labari ya iske en cikin gida baki d'aya da saida gaban Ammah ya fad'i sbd tuno wani irin hali d'iyar ta zata shiga idan taji wannan labari kishiya da rana t'saka!!!! Addu'a take Allah yasa kar tazo gidan amma kuwa sai addu'arta bata karb'u ba,domin kuwa a lokacin da ake t'saka da gulmace-gulmacen abin saiga ta da sallamar ta,tana jan cikin ta da yayi wani irin girma ba kad'an ba da k'yar take ciccilla k'afafun ta.

Nan kuwa kowa keta faman binta da kallo ana zancen ta k'asa k'asa da yasa taji dik ta muzanta,don haka sai kawai ta tashi cikin jama'a zuwa d'akin Hajja da itama keta faman jimamin abinda ya faru cikin d'akin ta tare da tata tawagar.

Kwanciya tayi ta juya masu baya tana mai jin yadda zuciyar ta kwata-kwata bata da nat'suwa tinda ta tako kafar ta cikin gidan.
Inda take ta faman k'iran wayar Mijin ta amma ansa d'aya ake bata shine "no answer"   Haka nan ta wuni a kwance cikin rashin dad'in rai da kuma damuwar rashin samun mijin nata a waya da hankalin ta sosai ya karkata izuwa ga sanin halin da yake ciki.

Ammih ma da taji labari sosai taji gaban ta ya fad'i sabida sanin halin yaron nata da tayi ciki da bai,da kwata-kwata bashi da ra'ayin zama da mace sama da d'aya,tana kuma guje masa aikata rashin adalci da ranar lahira zai iya tashi da shanyayyen gefen jikin sa guda.

...……...……...……...

A b'angaren gidan Abbah kuwa...!

Bayan an gama cuku-cukun d'aurin aure kowa ya soma kama gaban sa,Abbah bai samu damar shiga cikin gida ba,saida ya tabbatar da ya gama sallaman bak'in baki d'aya,inda ya wuce part na Mami daya tadda cike yake da bataliyar ta na k'awaye...!!!!

"Aishatu ina su Mamana ne?" Abbah ya tambayi Mamy bayan sun keb'e a wani d'aki. "Ai kuwa suna can b'angaren Khadeeja tare da k'awayen ta." Ta basa ansa tana kallon yadda fuskar ke cikin damuwa da yasa ta gaza hak'uri ta tambaye sa abinda ya faru,ai kuwa tiryan-tiryan Abbah ya k'oro jawabi da yasa Mamy buga wani uban tagumi cike da t'sant'sar damuwa akan abinda kan iya zuwa ya dawo idan Ummi ta samu bayani!!

Ummi kuwa da bata jima da farkawa a bacci ba na can tare dasu Jiddah dake ta faman k'ok'arin ganin sun shirya ta amma sai iya shege take masu kan ita babu wanda zai tab'a mata fuskarta da wayannan abubuwan jagwalgwalen...!

"Bari na k'ira Uncle J wata k'ila idan shi yazo ya lallab'a ki zaki fi t'sayawa tinda nasan war haka an riga da an shafa fatiha." Wani dum gaban Ummi da tinda ta farka take cikin farin yayi sabida ambatar sunan Uncle J da Asmy tayi tana jin wani irin zafi har cikin ranta batare da sanin dalilin hakan ba.

Abbah ne tare da Mamy suka aiko aka zo masu da Ummi zuwa part nasa da babu cikowar jama'ah...!!! Nan suka zaunar da ita tare da mata nasihar karbar rayuwar ta a dik yadda tazo mata,sabida ubangiji da yasa hakan ya faru shi yafi ta sanin asalin dalilin hakan.

A lokacin da Ummi taji sunan wanda aka aura mata maimakon Uncle J kad'an ne ya hana bata mik'e ta taka rawa ba,sabida t'sananin farin cikin faruwar hakan da kuma jin dad'i...! A gefe guda kuma wani irin t'soro ne ya kamata,yanzu idan shi Zulaym Shuwa d'in ya tab'ure masu kan shi bai son ta yaya kuma makomar rayuwar ta zata zamtoh?! Wanda hakan yasa nan take taji dik murnar ta ya koma ciki,saima kukan da ta sakar ma su da sunan na rabuwa da Uncle J ne,nan kuwa su basu san na wani abin ta daban bane...!

...……...……...……...

B'angaren Uncle J kuwa tare da wasu abokan sa suka kai matar tasa dake sume tana ta faman zubda jini asibiti cike da t'sant'sar tashin hankali da nan da nan aka wuce da ita emergency aka shiga bata dik wasu taimakon da suka dace da condition d'in da take ciki!

Inda aka samu daidaiton numfashin ta,tare da sank'ama mata jini tare da drip sai kuma allurar bacci(😆yasin halin india ne wagga abu,wata ma tsaf sai ta kashe kanta akan saurayi sabida gidahumanci😆).

Wajajen k'arfe takwas na dare Yaya ya k'ira Jafar kan yazo ya same shi tare da matar sa da yasa don dole aka rubuta masu sallama a daren bayan dogon gargad'in gujema abinda zai famar mata da ciwon ta zuwa gidan nasu!

Anan ya tadda Yaya Babba,Babi,Dad,AMADU,Hajja,Ammih,Ammah,Mom,Um-asmy sai Yaya tare da Husnah dake wajen k'afafun Ammah tana ta kallon Yaya da sai yanzu ta sashi cikin idanun ta wanda kuma idan ba gizo idanun ta ke mata ba,gani take kamar dik yayi zuru dashi lokaci guda...!

*vote*
*comment*
*share*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now