Part 9

80 8 0
                                    

*RIJIYA TA BADA RUWA...!!*
    
                                 

           *charpter 9*

********Ba ita ta farfad'o daga gajerar jinyar da ta fada ba,saida tayi kwana biyu tana bacci sanadiyyar allurar data ke ansa wajen likitocin,inda Mamy ce ke kwana da ita tare da Abba da shima sam yace bai san zancen tafiya gida ba da Mamy tayi masa,sabida hankalin sa bazai taba iya kwanciya ba shi yana can gida yarsa na nan kwance rai a hannun Allah.
Musty ma dai kusan zance dashi ake jinyar zulaykha,domin kuwa har ya janye fushin da yake sanadiyyar abinda Abba yayi masa a wancan ranar,sabida soyayyar da yake ma Zulaykha tin kamin ta gama sanin ciwon kanta.

Inda aminan arziki dama na tsiya suke ta faman kai kawo zuwa asibitin sabida dubiyar mara lafiya,Mamy ma dai yanzu tayi sanyi sabida rashin lafiyar ita Zulaykhan,wanda kuma Musty ne idan ya samu lokaci yakan dan laika ma'aikatar tasu domin ganin abubuwan dake wakana bisa ga umarnin da Abba ya basa.

Tinda ta farka kuwa ta rama sallolin da suka kufce mata baki d'aya,wanda kuma jikin da sauki sosai,su Abbah sunyi-sunyi ta fad'a masu damuwarta amma ta k'ek'ashe k'asa tace ita babu abinda yake damunta,kawai ciwo ne daga Allah.Ba dan su Abbah sun yarda ba,saidon babu yadda zasuyi suka bar zance sabida likita ya shaida masu akoi abinda yake damunta daya sa hawan jini ke k'ok'arin kamata.

Sai da Zulaykha tayi sati guda cif cif a asibiti,kamin aka sallamo su suka koma gida,tare da rakiyar y'ar gidan aminin Abbah mai suna *JIDDAH*.
Wacce ta kasance matsayin babbar aminiyar Zulaykha,dikda kasancewar bada ko yaushe suke tare ba!
Jiddah kyakkyawar yarinya ce mai sanin ya kamata,sam itama bata da wani rawar kai a rayuwarta irin na y'an matan zamani,wanda hakan ne ma yasa amintakar su tazo daya tare da Zulaykha.

Bayan kwana biyu da komawar su gida.

"Wai ke matar nan miyasa kika wani dage sai kin tafi gida tin daga yau? bacin kuma Dad yace maki sai kinyi sati kamin ki koma gida." Zulaykha ce ke wannan maganar da take nade cikin bargonta,irin na duniyar kule,kanta ne kawai ke waje take ma jiddah magana dake kokarin saka wata doguwar rigar Zulaykha na shadda.
Ba tare da jiddah ta juyo ba itama tace "Allah kuwa baki isa ba ma yarinyar nan! Ai naga kin riga da kin gama warkewa daga ciwon naki da zaki wani ce sai na kai sati a nan,bacin kuma nasan Mom na can gida tana fama da kewata."
jiddah ke wannan maganar cike da jin dadi sabida tunowa tayi da mahaifiyarta da a kullum bata gajiyawa da ita ta ko wanne fanni.

Kanta dake waje Zulaykha ta idasa shigewa dashi cikin bargo, ba tare data bama jiddah ansa ba,wanda hakan kuma baisa jiddah tayi wani tunani daban ba,tana gama saka kayanta had'i da daukar jikarta tare dasu wayoyinta ta karaso bakin gadon da Zulaykha ke kwance,ta daddage ta lafta mata duka ta fice daga dakin da gudunta tana fadin ladar jinyarki danayi na fanshe tinda ke naga baki da niyya.
Alamu dai bayau suka sama irin hakan ba,kamar yadda dabi'ar abokai take na kaiwa aboki duka a un-espected.

Jin alamar jiddah ta fice daga dakin ne, ya sa ta mikewa zaune bayan ta yaye bargon daya lullube mata jiki,ta jingina bayan ta a jikin allon gadon nata,kanta a sama wasu irin zazzafar hawaye na zubowa daga cikin idanunta,alamun ta jima tanayin kukan a tin lokacin data lumar da kanta cikin bargo sabida jin Jiddah ta anbaci Mom dinta,itama tunowa tayi da tata mahaifiyar da batasan a wace duniya take ciki ba.
Abba ne ya shigo cikin dakin bakin sa dauke da sallama ya tadda yar lelen nasa cikin wannan yanayin daya masifar d'aga masa hankali.

********A kusan lokaci daya Yaya da Waleed suka shigo d'akin,hannunsa rik'e da wata laida dake d'aure da wani garin magani a cikinsa,hankalin sa a mugun tashe,yayo zuwa inda Ammah da Husnah suke,wanda har zuwa lokacin Husnah bata bar rawar darin da take ba,harma ya zarce misali.

Mika ma Ammah laidar dake hannun sa yayi,a lokacin da yayi nasarar raba jikin Ammah da ita Husnah,kamar jinjira haka nan ya dauke ta zuwa kan gadon Ammah yayi mata masauki amma taki sakin sa,saima sake shigewa jikin sa da tayi.

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now