Part 19

71 11 0
                                    

*RIJIYA TA BA DA RUWA...!!*

*©️OUM_MUMTAZ✍️* 
        

           *charpter 19*

******** 'Bangaren ango da amarya kuwa sosai suke rakashewa suna zuba amarcin su babu ji babu gani! Kowa k'ok'ari yake wajen ganin ya faran ta ma d'an uwan sa rai ta hanyar t'saftatacciyar soyayya da babu algus,wanda suka gina zaman rayuwar auren su bisa ga koyi na fiyayyen halitta Annabi Muhammad(S A W).

Sam Yaya bai son abinda zai tab'a masa ASMA'Un sa ko na misk'ala zarratin! Wanda itama haka nan take,dik wasu hakkokin sa daya rataya a wuyan ta tana k'ok'arin sauk'e wa kamar yadda shima bayyin sanya sai na d'an abinda ba'a rasa ba!

Sannan kuma a lokuta da dama su Hidaya tare da sauran yaran gidan nasu dama na gidan y'an uwa kan kawo masu ziyara,haka nan suma suna kaima y'an uwa da abokan su nan Abuja da Suleja ziyara ba kad'an ba.

A gefe d'aya kuma har an riga an gama settling na auren Anty khadeeja da Dad yayi masa zance nan da wata d'aya.

Mat'salar Yaya guda d'ayace!!! Sam sam bashi da sakin fuska ga yaran y'an uwa ko kad'an! Dik inda yaro koman k'ank'antar sa yakai ga son Yaya ya d'auke sa to kuwa tabbas karya ce,sai ma dai kora su yana daddaure fuska,wanda hakan ya sa yaran ke shayin sa ba kad'an ba!
Wanda dama hakan ne shi ke had'a sa da Anty khadeeja da suka kasance abokan shawarar junan su tin suna k'anana har kawo girman su!

Ita akoi ta da son jan na k'asa da ita a jiki,bacin shi kuma sam-sam ba haka bane,a lokuta da dama takan fad'a masa cewa, "A yadda kake hantarar mana yara kaima zan so naga yaya zakayi a lokacin da ka haifi na kanka idan aka nuna ba'a yin su a gaban idanun ka!!"

Idan yaji hakan kuwa sai dai yayi dariya kawai ba tare daya bama maganar tata mahimmanci ba,inda Yaya babba ke d'aure masa k'ugu yace, "Kar a takura ma mai sunana fa." Hakan na damun Husnah da itama Allah ne ya d'aura ta akan sa tin tana k'ank'anuwar ta bata shak'u da kowa ba kaman sa,amma yanxu auren nan da sukayi yasa ta jin dad'i tana ganin komai ya kusa zama dai-dai,idan har ya haifi d'an kansa tana da tabbacin zai san mahimmanci da kuma dad'in yara ba kad'an ba,sabida babu wanda zai haihu yace "ba ya son abinda ya haifa"

Abin farin cikin daya iske su kuma a yanzu shine shigar k'aramin ciki da Husnah ke dashi,wanda kowa ke cikin farin ciki da wannan kyauta amma banda Yaya daya so a zubda cikin wai don sabida bai shirya haihuwa ba,yafi son sai sun kai irin 5yrs da aure d'innan,wanda hakan ya mugun b'atama Husnah rai amma ko kula sa ba tayi ba,ta kuma riga da tasa a ranta bai isa yace zai zubdar mata da ciki ba sabida ganin take-taken sa hakan yake so ayi,gashi kuma ita bata san ko iya wannan bane kad'ai nata kwan a duniya da Allah yayi mata yakai ta ya baro ta akan wani shirme na social life wai,wanda take da tabbacin koman daren dad'ewa idan akace yau bata haihuwa koman son da Yaya kanyi mata sai ya sake dank'aro mata kishiya,wanda ita kuma sam bazata so hakan ba,kasancewar ta mace mai zazzafar kishi akan Yayan nata tin bata kai haka ba.

Yaya kuwa ganin baiga fuska bane yasa shi shafa mata lafiya,amma kuma kullum cikin yin muzurai yake kamar wanda akayiwa laifi yana daure ma Husnah fuska ba kamar a baya ba,kuma dik wannan iya shegen da yake t'sulawa babu wanda ya sani daga shi sai matar tasa da ita kuma bata so asan da zancen sabida Yaya gani zayyi kamar takai karar sa ne,wanda kuma sai da Ammah ta hane ta da fidda sirrin t'sakanin ta da mijin ta idan hakan bai kama ba.

Wannan canjin da take gani daga mijin nata kuma sosai yake damun ta,amma bata san ta yadda zata masa bayani da zai fuskanci gaskiya ba,dik dama tana da tabbacin sarai yasan abinda yake so suyi d'in haramci ne amma yake son takewa sabida son zuciya da kuma d'aukar zugar abokai da suke fada masa idan ya sake ya fara haihuwa tin daga yanzu ya gama t'sofewa kamar wanda t'sufa da rashin t'sufar a hannun su yake.

******** Sam Alhaji ba mutum bane,gagarumin mat'safi ne fiye da kima daya fito daga jinsin aljanu,wanda wasu aljanun da kan su na sara masa a wannan fannin!
sannan kuma dik wannan bidirin da yake na t'safi bai aiki da aljanu ire-iren sa sai da bil adama! Wannan ya tara gagaruman jahilai a karkashin sa cikin jinsin mu da suka d'auki duniya da abinda ke cikin ta da fad'i,sukan yi masa sadaukarwa na jinin iyayen su,matan su,yayan su,yan uwan su da kuma way'an da basu da alak'a domin yayi siddabarun sa dashi shi kuma yakan buga masu kud'in t'safi kamar na hauka cikin k'ank'anin lokaci!

Yayi aure da dama cikin jinsin bil adama suna haifar masa yara shi kuma yakan shayar da kansa jinin ki bacin kin haihu,inda daga karshe kuma sai ya fed'e ma jariri ko jaririyar da aka haifa masa yayi amfani da sassan jikin su wajen ganin ya inganta t'safin nasa ta yadda zayyi karko.

Kuma dik matan da yake aura kwad'ayi ne ke fusgar su izuwa gare shi domin ko bai zuwar masu a siffar wani abu mara kyan gani sai a siffar bil adama!
Baba rabi ma na d'aya daga cikin wannan matan daya bugu su a dalilin son abin duniya tin tana budurwarta,har kawo girman ta,wanda itama dalilin daya sa bai kashe ta tintini ba sai don bata tab'a haihuwa dashi bane wanda sam hakan bai cikin nasa t'sarin na t'safi, a ranar da mace ta cika sati guda cif cif da haihuwa yake idasa cika kudirin sa babu daga kafa balle kuma wani abu wai shi tausayi,kuma dik macen data shigo cikin wannan gida daga ranar zayyi mata formating na cikin wawalwarta ta yadda zama ta manta ita wacece ko kuma daga ina ta b'illo? suwa ta baro? Dik wannan sai ya tabbatar daya gama goge mata wannan haddar!

Batin Alina kuwa tin a ranar da aka haifo ta garin bincike-binciken t'safin sa aka tabbatar masa da cewa jinin ta,na mahaifiyarta da kuma na abinda zata haifa masa da kaf matan daya ke haihuwa dasu babu wacce zata haifa masa kamar yadda ita zata haifar masa,wanda kuma sune matakin sa na nasara na karshe da zai zama gagarumin mat'safi da dik duniyar aljanu zasu san da zaman sa,mai matik'ar girma da kuma iko.
wanda hakan yasa Alina tin tana k'ank'anuwarta yake bibiyar dik wani mot'sinta a tafin hannun sa,sai kuma abinda ya sake sashi farin ciki shine na ganin halin ta na kwad'ayi yasan bazai sha wahala ba wajen cimma burin sa,kasancewar a t'sarin kalar nasa t'safin sam-sam babu tilastawa,dan haka dik wacce yake aura ya kuma kashe ita ke kawo kanta da kafafun ta har inda yake,shi kawai nasa ya saye su ne da abin duniya kamar yadda ya sake saye zuciyar Alina a lokacin daya bayyana a gareta.

A daren ranar da suka gudu da Alina,a washe gari wannan ranar yasa aka ciro masa mahaifiyar Alina daga cikin k'asa,wacce a wajen duniya rasuwa tayi daren jiya d'in,nan kuwa basu san cewa hakan dik cikin set-up na Alhaji bane.

Inda ya keb'eta a wani d'aki yake shayar da ita with thick blood na bil adama tare da d'anyen nama! Wanda jiran wannan ranar yake domin ya idasa cika kud'irin sa akan Alina da mahaifiyarta tare kuma da yaran da aka haifa masa.

Tonon asirin da Baba rabi tayi masu kamin su cika kudirin su kan iya ruguza masu dik wani t'sare tsaren su,wanda hakan yasa suka yanke mata wannan danyen hukuncin,kaf cikin mutanen dake d'akin manya manyan k'asar mu ne dama wayan da ke mak'waftaka da mu idan aka d'auke ainahin Alh daya kasance shine boss nasu!!

(Kar na ja masu karatu dayawa,wannan shine tak'aitaccen bayani dangane da wannan Alhaji).

Sam Alina ta gagara mot'sawa daga inda take balle ta iya kaima mahaifiyar tata d'auki sabida d'ad'd'aure mata jijiyoyin jikin ta da wannan halitta yayi dake mat'sayin Alhaji da wai har tayi kwanciyar aure dashi!

Jikin ne ya fara karkarwa tana faman girgiza kanta a lokacin da taga Alhaji ya kafa bakin sa akan nonuwan mahaifiyarta dake kallon y'ar tata itama tana t'siyayar hawaye mai cike da t'sant'sar tausayin kanta da kuma y'ar tata da ba komai bane ya jawo mata hakan illah kwad'ayi dai!!

*vote*
*comment*
*share*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now