Part 27

64 8 0
                                    


*RIJIYA TA BA DA RUWA...?*

*©️OUM_MUMTAZ✍️* 

_WANNAN LITTAFIN TIN DAGA FARKON SA HAR K'ARSHEN SA NA SADAUKAR DASHI GA ~MSS FLOWER🌸🌸~ MARUBUCIYAR:_
~LAFAZI~
~AR SO~
~SARKI~
~GUMBAR DUT'SE~
_SON SO FISABILILLAH❣️💃🥰❣️❣️_                          
   
           *Charpter 27*

******** Ashe tin daren jiya ma'aikatan gidan da abin ya isa sukayi zaman meeting yasu-yasu,ta yadda zasu k'watar ma da kansu hak'k'in su na ganin an biya su albashin su da aka danne wata da watanni!!!
Hankalin su Mamy da Anty Khadee dake gida ba k'aramin tashi yayi ba,sabida ganin yadda suke ta faman rurrushe masu windows nasu cikin hargowa suna fad'in sai an biya su hak'k'in su ko su tada unguwar! Mamy batayi gigin k'iran wayar Abbah ba koda wasa,sabida tasan muddin indai yaji labarin to kuwa tabbas sun kad'e yau har buzun su yau kashin su sai ya bushe k'ik'ir,danna ma Musty dake office k'ira tayi,wanda shima ta jiyo sa cikin hargowa da hayaniya,sanadiiyar wirge wurgen da ma'aikatan keyi suma sai an biya su kud'in su sun tada zanga-zanga!!

Hankalin Mamy kam sake tashi yayi fiye ma da baya,ta rasa mai ke mata dad'i! Da kuma ta inda zata fara taren abin kamin Abbah ya ji labari! Anty khadee dake can ta kulle kanta a d'aki ita ta k'ira Abbah cikin tashin hankali ta shaida masa kan ga nan ma'aikatan gida nata faman faffasa dik wani abin da suka samu a gida kan sai an biya su hakkin su,wanda ita kuma bata san manufar hakan ba!!

A lokacin Abbah da Dad suna tare ne,Dad ne ya k'ira commisioner of police ya shaida masa kan yakai yaran sa gidan Alh Abdulwaali babu lafiya emergency,sbd yadda Abbah ma dik yabi ya rikice yama gagara mik'ewa ballantana yayi yunk'urin yin wani k'wak'k'waran abu!
Tare da taimakon Dad suka fito daga office d'in yana ta faman rirrik'e shi,wanda hakan ya jawo hankulan ma'aikatan kamfanin da aka samu wanda ya kaima Ummi rahoto kan gacan Abbahn ta ya gagara tafiya sai da taimakon yallab'ai Yusuf kamar baya cikin hayyacin sa.

Ai kuwa da gudu gudu sosai ta fito daga office d'in nata,wanda ba tare data ankare ba dogon takalmin dake k'afarta taja ta sai ji kake timmmm!! Wanda hakan yasa ta callara wani uban ihu cike da t'sananin azaba da ya sake hargit'sa ma'aikatan baki d'aya! Abbah dake can tare da Kabeer da yazo ya shaida masa kan abin da ke faruwa acan ma'aiakatar tasu ne ya sake d'aga masa hankali fiye da tunanin mai tunani,sai kuma ihun d'iyar tasa da ya karad'e illahirin harabar ma'aikatar tasu,bai san lokacin da ya k'arasa wajen ba ma ya ciccib'eta a mugun gigice kansa na barazanar t'sagewa gida biyu.

Dad ne ya amshe ta ya sata cikin mota ya umarci su Kabeer su wuce hospital da ita,shi kuma ya kamo Abbah suka fad'a mota zuwa ma'aikatan Ummi d'in domin jin ba'asin zanga zangar!!! Masu t'saron Abbah na take masu baya,da dik wanda ya gansu a lokacin sai ya kaice masu a hanya sabida yadda suke banbara uban gudu kamar babu gobe!

A lokacin da suka isa ma'aikatar hankalin Abbah da shi kansa Dad d'in idan yayi million a ya sake tashi k'warai da gaske,domin kuwa sun tarda matasan nan sunyi b'arna ba kad'an ba,wanda hakan yasa Dad sake k'iran commisioner of police kan a sake aiko masu da yara nan ma sabida ga abinda yake faruwa!! Dik yadda su Abbah suka so suyi calming na mutanen nan amma fir suka k'i,saima hayayyak'o ma Abbah da sukayi,kan ai shine ya d'aure ma y'arsa gindi take abinda taga dama yau idon su idon ta sai sun koya mata hankali!! Banda karkarwa babu abinda jikin Musty keyi,sabida yasan tabbas yau kam dubun su ta gama cikewa fes-fes daga shi har Mamyn nasa data tinzira shi yake wannan aika aikar.

Abbah kuwa sam k'wak'walwarsa ta toshe...yama gaza gane inda zantukan nasu suka sa gaba...masu kama da k'anzon kurege!!!
Isowar y'an sandan da suka fara k'wamushe su ne yasa wajen sake b'arkewa da hayaniya fiye da baya,a kuma lokacin ne Abbah ya samu nasarar saka Musty dake ta faman had'a zufa cikin idanun sa! Dad ne ya umarci Musty d'in tare da wasu ma'aikatan da babu su a masu aika aikar su biyo su,da kuma wasu y'an sandan zuwa cikin wani babban hole da aka tanade shi musamman domin irin wannan had'uwar ta gaggawa idan ya kama.

Wani daga cikin ma'aikatan ne ya shaida masu abinda ke faruwa a lokacin da Abbah ya buk'aci jin ta bakin su!!! "Wato yallab'ai a gaskiya abinda ake cikin wannan ma'aikatar kwata kwata baya dacewa, domin kuwa ita madam Zulaykha a watannin baya da suka gabata wajen wata takwas zuwa tara kenan ta rage ma dik wani ma'aikaci dake kamfanin nan salary wajen kaso 15 cikin d'ari, wanda hakan ya mugun d'aga mana hankali muka tinkari yallabai Mustapha da maganar sabida sak'on daga wurin sa ya iske mu, amma sai ya bamu hak'uri tare da tabbacin insha Allahu zai san ta yadda zai biyo mata har ta biya mu dik wasu kudaden da ya zamtoh hakkin mu, to a gaskiya yau da gobe tafi k'arfin wasa, tin muna jurewa muna magana ta k'asa-k'asa har hakurin mu ya fara gazawa muka fara tunanin hanyar da zamu bi wajen ganin mun karbo hakkin mu, tinda kullum yallabai cikin shaida mana kwana kusa zasu biyamu abin yaci tura,wanda hakan ya fusata wasu daga cikin mu suka tada zanga-zanga kan sai an biya su hakkin su ko kuma su tada wajen kowa ma huta...……"

Shuru wajen ya d'auka na wasu y'an dak'ik'u, wanda a dai-dai wannan lokacin da masu karatu zaku t'saga jikin Musty to kuwa babu abinda zaku gani sai magudar zawo a wando sabida tashin hankali🙈....Abbah kuwa ransa idan yayi dubu a dai dai wannan lokacin ba karamin baci yayi ba,wani shashi na zuciyarsa na k'ok'arin k'aryata abinda aka fada akan yar tasa sabida sanin halin ta da yayi ciki da bai,wanda kuma wani b'arin na fadi masa da cewa ai dan yau ka haife sa ne baka haifi halin sa ba!!! Wanda kuma a gefe guda Dad ma ya t'sunduma tunani ne cikin wannan lamarin ne gadan gadan.

'Dan sandan dake daukan details kan zantukan da ma'aikacin keyi ne ya sake jefo masa tambaya, "ina shi yallabai Mustaphan naku yake yanzu??"  "Gashi nan ranka shi dade." Kallo daya police din yayi ma Musty ya hango tsagoron rashin gaskiyar dake tattare da yaron! Cikin t'suke fuska police d'in yace, "Mallam Mustapha ko zaka iya yimana bayani dalla-dalla dangane da abinda ya faru ta yadda zamu fi fahimta???" Zufa ne sharkaf ya sake jik'a rigar Musty ya fara zuba i ina yama rasa ta inda zai fara bayani!! Wanda hakan yasa  daya daga cikin police din kallon Abbah da ya lula duniyar tunani da kuma Dad dake ta faman kallon Musty cike da nazarin sa yace, "yallabai zamu wuce da wayannan can offishin namu,sannan kuma muna da buk'atar ganin ita mamallakin kamfanin sabida muna so muyi mata wasu y'an tambayoyi dangane da case dinnan! Don haka yanxu zaku tafi da wasu daga cikin yaran mu suzo mana da ita,mu zamu wuce da wayannan din"

Tsakanin Abbah da Dad babu wanda ya musa,inda suka wuce tare da motar police guda sauran kuma suka kwashi su Musty bayan an rufe gate na ma'aikatar zuwa police station......!

………………

Asibiti su Abbah suka nufa,wanda suka tarda har zuwa lokacin likitoci basu fito akan ta ba,sabida buguwar da kafarta tayi hakan yayi sanadin yi mata karaya cikin kashin ta. Kabeer dinma dashike dashi za'a tafi station din sai ya zauna asibitin tare da yan sandan,kan idan aka gama da ita zasu wuce aje a karashe case din!
Wanda daga nan kuma su Abbah suka maida akalar tafiyar tasu zuwa can unguwar Maitama domin gano yadda Al'amarin can d'in yake!
Acan kuwa abinda ya faru tin bayan shaida ma Abbah abinda ya faru da Anty khadee tayi shine……✍🏽

*vote*
*comment*
*share*
  
*OUM MUMTAZ✍🏿*

RIJIYA TA BA DA RUWA???? Where stories live. Discover now