Ni Da Prince 51-55

12.8K 388 12
                                    

11/13, 10:47]

☄☄☄☄☄☄☄
💥 *NI DA PRINCE*💥
☄☄☄☄☄☄☄

*NA AYUSHER MOHD*

NO.5⃣1⃣

Zeena tazo sai dai duk yanda ta roki Salman akan yaci abinci amma yaki, tai fad'an har ta gaji, shikam yama dags akan ta rakashi agwada jininsa su tabbatar zai iya bata, a d'eba asa mata.

Zeena ta kalleshi tace " haba Salman mai yasa kake haka? Kabari gobe in an kira 'yan uwanta sunzo sai a gwadaso asamu wanda yai a kara mata, amma kai baka da lafiya ina kai ina bada jini? Sannan gashi sam kakicin abinci."

Salman ya kalleta yace " Aunty zeena har dake? Nad'auka ke ba halinku d'aya dasu ba, taya zakice gobe in 'yan uwanta sunzo, Salma matatace kuma saboda wani abun dabai gagareni ba bazan nuna mata nafisan kaina akanta ba, abinci kuma inkinga naci abinci to tabbas naga matata taci." Yanakai nan ya fita, Zeena tausayinsa ya kamata, wani irin so Salman kema Salma haka? A da taga ko kallo bata isheshi ba, yaushe abu ya juya haka?.

Salman da kanshi yaje lab d'in suka gwadashi sun tabbatar O+ gareshi kuma zai iya bata, wucewa yai gun likita yace "tashi muje ko?"

Likitan yace "Yarima dan Allah....."
Cikin fad'a Salman ya katseshi yace "Karka bata min rai, inace inason abu to kamin kafin ranka ya b'aci, nagaji da ganin matata a kwance."

Likitan yace "kayi hakuri ranka ya dade amma matarka badan jini bane taki tashi."
Salman yace " Naji, amma wuce muje inka kara mata jinin sai nu jira in ta wuce hours d'in daka fad'a hmm bansan kuma mai zan ma ba."
Salman ya juya, da sauri likitan ya fito sukai shigo da kayan aiki d'akin, an saita komai sai da ba'a fara ba mai martaba ya iso shida waziri.

Salman na ganinshi ya had'iyi wani abu tare da kara d'aure fuska, Sarki ya karaso kusa dashi, waziri ya kalli Zeena dake gaida Sarki yace inkin gama kowa ya fito yabasu guri, tace to.

Kowa ya fita yabarsu su biyu sai Salma dake kwance, Sarki ya kamo hannun Salman ya rike yace "Salman na tsorata danaji ance bakada lafiya na d'auka kaima rasaka zanyi."

Salman ya kalleshi idanshi yai jaa, dasauri ya maida kanshi gefen da Salma take, Sarki yace " Salman meyasa baka sanar dani larurarka ba? Ina zaune bansan halin da d'ana yake ciki ba."
Salman ya kalleshi yace " Ina zaka sani Abba? Tunda mukamin ka yafini daraja? Tunda kake dani ka taba tambaya ta yana tashi? Meke damuna? Naci abinci? Bani da wata matsala dake damuna?"hawaye ya zuboma Salman a ido yacigaba" Kun rufe mutuwar Ummana saboda san mulki, kun turani wata kasar dan bazaku iya kula dani ba, sannan yanzu Abba katambayeni wai zancen ciwo na? Ban fad'ama ba?"
Ya share hawayen dake zubo masa yace " kasan wace irin rayuwa nayi? Kai dai kullum kana zaune akan kujerar mulki sai abinda aka fad'ama."
Salman na zuwa nan ya runtse ido, hawaye suka kara zubomai ya share tare da kallan Salma, yace "zan iya jure komai amma banda a tab'a matata."

Sarki da tunda Salman yafara magana kwalla ta cika taf a idanunsa yasani sarai abinda Salman ya fad'a duk gaskiya ne, amma ya zaiyi? Tunda haka mulki ya gada.
Kafad'ar Salman ya dafa, ya d'ago ya kalleshi cikin tsananin tausayin d'an yace Salman na sani duk wani abu dake damunka laifinane na sani amma dan Allah Salman ka cirema zuciyarka komai ko ka samu nutsuwa, kaduba matarka, ciki gareta ka taimakeni Salman ka cire komai aranka kafin d'anka ya taso da kiyayyata, Salman kayi hakuri akan duk abubuwan dana maka, nasani sarai abin na damunka amma zuciyata inta ganka sai inji tausayinka bazai bari in tada maganar ba."
Salman ya kalleshi yace " So nake ka bani izini ind'au matata in bar gidan, dan banasan zama a cikin gidan, nafisan inda zamuyi rayuwa kamar kowa nida abinda za'a haifarmin."

Sarki ya kalleshi tare da jijiga kai, yace Salman banda wannan, zan iyama komai Salman amma bazan iya barinka nesa dani ba, bayan kaine magaji na."

NI DA PRINCE  Where stories live. Discover now