Ni Da Prince 56 - 60

11.1K 356 9
                                    

💥 *NI DA PRINCE* 💥
☄☄☄☄☄☄☄☄
*NA AYUSHER MOHD*
No. 5⃣6⃣
Sun fito shida Farha, ko kallansu bai ba ya wuce
tare da cemata kisameni a mota, Farha ta fito
janye da jaka, ta kuma rataya handbag d'inta, ta
karaso kusa da Fulani tace "Fulani ni zan wuce,
amma zan d'inga lekowa."
Fulani tace "ina zaki?"
Farha tai shiru sai kuma tace " nikaina bansani
ba, yayana ne yace infito." Fulani tai dariya tace
"lalai Farha, kawai dan Salman yace ki fito
shikenan sai ki fito?" Farha ta mike tare da kallan
Ishaq tace " na wuce."cikin rawar murya Ishaq
yace to.. Sannan ta kalli fulani tace "nagode
sosai." Ta juya tai waje Fulani ta bita da kallo
tace "maza, hmmm Allah dai yasa ba hotel yake
shirin kaita ba." Sai kuma ta mike ta saki dariya
ta matso kusa da Ishaq tace "Allah yasa hotel
d'in zai kaita, da alama ya kamata ka tura mana
wannan mai kula da harkokin Salman, ya
tabbatar ya d'auko hotonsu inzasu shiga hotel
d'in."
Ishaq ya kalleta yace " Umma na kula baki damu
da harkata ba, kawai ke kanki kika sani, burinki
kawai inzama Sarki, baki damu da halin da nake
ciki ba."
Fulani ta kalleshi tad'anyi siririn tsaki tace "
maganar Salma ce?"
Ishaq yace " har da ita."
Fulani ta dafa kai tace "oh God! Ishaq dan
kanasan abu nizan je in jawo maka hankalin
abinda kake so? Kaje kayi duk abinda kaga
dama." Tai maganar cikin gatse, Fulani ta d'auka
zai bata hakuri, amma sai jitai yace " yauwa
Umma nagode kwarai." Yanakainan yai waje da
saurin shi, tana kiranshi ko kulata baiyi ba.
Tace " Oh God! mai yaron nan yake tunani?"
Sun d'au hanya Farha sai jansa take da hira,
shidai sama sama kawai yake amsa mata, can
yace "Farha?" Jin yanda ya kirata yasa jikinta yin
sanyi, tace " Naam"
Salman yace " I won't ask you to forgive me, dan
nasan abinda nake shirin yi shine dai dai, koda
kuwa zaki kulaceni, ki zageni, it won't matter,
nafiso na zama bad guy a kan harkata dake,
bazan bari ina kallo halayenki su canza ba, bayan
nasanki sarai."
Farha jikinta yai sanyi ta kuramai ido, tarasa
mezatace, batai magana ba taga sunzo hanyar
airport, kallanshi tai cikin tsoro da mamaki tace "
yayana nasani nayi ma laifi, bai kamata nayarda
har nasama maganin bacci ba, amma yayana this
is not right, karka wulakanta san danake maka."
Hawaye ne ya zubo mata ta share.
Salman shikanshi tausayinta yake, yasani bai
kyauta ba amma bazai bari yana kallo takoma su
fulani ba.
Baice komai ba ya shigaba da tukinsa, Farha kuka
take sosai, ya daure yace" garin nakune bakya
san zuwa kome?" Farha haushi ya kamata ta
d'auka in tana kuka zai tausaya ya fasa tace"
nikaine banasan na rabu da gani." Salman ya sa
signal, yace " Farha kije ki nutsu kiyi tunani, me
kikeso?" Farha ta share kwalla tace " ni
yarinyace? A iya sanina ko matarka na girmeta
amma kace min ban masan me nake so ba?"
Salman ya karasa ciki, ya kira abokinsa, Farha
idanta yai ja, kana ganinta kasan taci kuka,
Salman bai kara mata magana ba, itama haushin
sa yasa taki mai maganar, sai dayaga sun shiga
check out sannan ya juya ya hau mota.
Waya ya d'auka ya mata transfer na kud'i 100
thousand, sannan ya ja mota yai waje.
Ishaq kam bangaren Salma ya nufa direct, sai
wani gyara kwalar riga yakeyi, yana shiga ya kalli
bayin gun yace "Salma fa?" Hanne tace tana ciki.
Ishaq ya kalleta yace " an bani sako ku jira a
waje bari in shiga ciki."
Yana shiga ya saki labulan falon ya fara kallon
part d'in, randa yafara zuwa dayake fada ne
yakawoshi bai kalla dakyau ba, amma irin nashine
kawai dai ya kula furniture's d'in nan sunfi nashi,
d'akin daya tuna Salma ta fito daga ciki wancan
zuwan ya karasa tare da yin knocking.
Salma dake zaune tana gyarama Salman
wardrobe yasa ta mike a hankali tai kofa, ta
bude.
Ganin ba kowa yasa ta fito falon sosai, Ishaq
dake tsaye jikin labule yai sauri ya shige d'akin,
Salma ganin ba kowa yasa ta koma d'akin tare
da rufowa, sai dai batasa key ba.
Tana zuwa wajen gado taji an rungumota ta
baya, murmushi tai tace " My Prince dama
kaine?" Jin kanshin bana Salman ba gashi yayi
shiru yasa cikin mamaki ta kai hannunta kan
hannunsa dake cikinta, inaaaa ba hanun Salman
bane, da karfi ta fizgeta juyo cikin tsananin tsoro.
Wazata gani? Ishaq? Tsoro ne ya kamata cikin
rawar murya tafara baya baya tanacewa " yarima
menene hakan?"
Ishaq ya matso yace " Salma please ki taimakenk,
nikad'ai nasan me nakeji in na ganki, Salma zan
mutu saboda ke."
Salma tace" me kake fad'a? Kamasan me kake
fad'a? Matar kaninka ce nifa? Ko ba matar
kaninka bace ni ai da kunya ka kalli mace
kad'inga mata zancen banza."
Ishaq ya fara matsowa, Salma kam zuciyarta
bugawa kawai take, wayarta ta hanga dake kan
madubi ba damar kiran Salman, ganin yanda
Ishaq ke tahowa yasa cikin tsoro ta d'au pillow
ta tare gabanta, sai dai tana cikin matsawa sai
jinta tai a bango, duka kawai take kaiwa da pillow
cikin fad'a tana cewa "ka fita, zan sa ihu fa?"
Ishaq kam sai daya karaso, ya rike pillow d'in
tare da fizgewa da karfi ya cillar dashi, hannunta
yariko da karfi, Salma ta kaimai cizo, amma ina
ko ajikinsa, ihu tasa sai dai bataga kowa ba, ihu
take sosai, ga Ishaq ya dage so yake yakai
bakinshi nata, sai cemata yake " Salma
kitaimakeni kamar yanda Allah yataimakeki."
Salma ganin yakusa kai bakinshi nata yasa ta
kwallama Salman kira da karfin gaske, jisukai an
bude kofa da karfi kamar za'a balla, Isahq6 ya
juyo dan yaga ko wani d'an rainin hankalin ne.
Salma kam kuka take sosai, Salman ya tsaya a
jikin kofa kamar zaki, idanunwashi sun canza
kala, fuskar nan a murtuke, a hankali Salma ta
bud'e ido, ganin Salman yasa ta fizge hannunta
daga gun Ishaq daya zama gunki, jikinsa sai
tsuma yake, itakam da gudu tai gunsa ta
rungumeshi tana kuka.
Salman kallan ishaq kawai yakeyi kallon dashi
kad'ai yagama tsorata Ishaq jiyai har hanjinsa
kad'awa suke, yama rasa me zaiyi, gashi bai
cinma burins ba, amma ya d'auka hotel suka tafi
da Farha.
☄☄☄☄☄☄☄☄
💥 *NI DA PRINCE*💥
☄☄☄☄☄☄☄☄


NI DA PRINCE  Where stories live. Discover now