Page 30-31

273 13 1
                                    

🍁🍁🍁
       *DIREBAN GIDANMU*
         🍁🍁🍁

_*by SaNaz deeyah*_👄

'''Dedicates 2 Mrs Xerks & Safnah luv'''

*_Kwana biyu kunjini shiru,wlh 'yata da cousin d'ina aka kwantar a asibiti_*
   _muna barar addu'arku_

_Wannan Shafin sadaukarwa ne gareku masoyana😍na san kun matsu nayi typing._

30

Da sauri Muhasin ya k'arasa ya d'agata yayi waje Momma na biye dashi.

Ganin idon Aliyu duk abinda ya faru, ji yayi kamar ya shak'e Muhasin saboda tsananin kishin Janan da yake.

           **********

Ta d'an goge guntun hawayenta bayan ta ji irin tarbar da iyalan Momma suka mata.

"Ba wai shawararku nake nema ba,na gabatar da ita ne a matsayin 'yata a gareku dan karku sakata a wani matsayi na daban daga yau matsayinku d'aya da ita a gidannan" Momma ta fad'a rai a b'ace.

"Wallahi ba'a isa a kawo mana wata haka kurum ace ta zama 'yar uwarmu" Zainab ta fad'a tare da tashi ta wuce ta bar falon.

Muktar ma tashi yayi yana gunguni ya bi bayan Zainab.

Momma cikin b'acin rai ta kalli Humaira tace "kema rashin kunyar zaki min?"

Itama Humaira ranta a b'ace take kallon Momma tana fad'in "taya zaki d'akko mutum kawai kice wai zata zauna a gidan nan"

"To gidanku ne ko gidana?"

Babban d'anta Umar yayi saurin cewa "gidanmu ne Momma saboda muke da gadon gidannan"

Baki kawai ta saki tana kallonsa cike da mamaki.

Haka rayuwar gidan Momma take duk kanin 'ya'yanta sun rainata Muhasin ne kad'ai ya fita zakka a cikinsu hakan ya samo asalina ga irin gatan da tayi musu fiya da misali.

Umar shine babba,yana da mata  da 'ya'ya biyu kuma a cikin gidan part d'insa yake.
Muhasin shine na biyu baiyi aure ba amma dai yana shirin yi,sai Muktar saurayi yana l3,Zainab tana l1 sai Humaira itace Auta tana Ss1.

Mahaifinsu ya dad'e da rasuwa tun Humaira na 'yar shekara 3 a duniya Momma itace gatansu babu abinda suke nema su rasa daga gareta tun mahaifinsu na da rai yakan ce mata wannan ba gata bane tana lalatasu ne kawai,amma sam bata yarda.

         ********

Momma na zaune a gefen gadon ta zuba uban tagumi,Janan na gefenta tana mamakin yadda akayi yaranta har suka rainata haka.

Zamewa tayi k'asa ta durk'ushe gaban Momma tace
"Ina neman alfarma a gareki"

'Dago ido tayi ta kalleta tare da janyota tana fad'in "haba Janan taya zaki tsugunna har k'asa dan kina neman alfarma"

Hawayen daya so zubo mata ne tayi saurin mak'aleshi tace "bakomai! Dan Allah ina so ki barni in tafi saboda ki samu zaman lafiya keda yaranki"

"Karki damu Janan ko ki tafi ko karki tafi haka halinsu yake ba fasawa zasuyi ba"

"Amma........"
"Ya isa Janan pls karki damu kinji"

Haka Momma ta jata ta nuna mata d'akin da zata zauna.
'Daki ne daya tsaru da duk wani kaya na bedroom sai toilet a gefe.

Haka rayuwar Janan ta cigaba da tafiya a gidan,Sam bata jin dad'in zama da 'yan gidan idan ba Muhasin da Momma ba.

Haka ta daure ta cigaba da renon cikinta cikin k'unci da b'acin rai.

DIREBAN GIDANMU COMPLETE✅Waar verhalen tot leven komen. Ontdek het nu