34-35

301 11 3
                                    

🍁🍁🍁
      *DIREBAN GIDANMU*
      🍁🍁🍁

_*by SaNaz deeyah*_👄

'''Dedicated 2 Mrs Xerks & Safna luv'''

_'Groups ina jindad'in comments d'inku.Nagode da yabo,da kuma k'aunar da kuke nuna min....much luv😍😘_


34

Kallon kallo suka tsaya yi dan shima mamaki yake da ya ganta a wannan yanayi.

Juyawa tayi da sauri da niyyar barin gurin yayi saurin cewa "Janan".

" ka santa ne?" Abbas ya tambayeshi.

"Janan d'ina ce fa"

Gabanta ya cigaba da fad'uwa tana tafiya zani na hard'e ta,yayi saurin shan gabanta.

"Janan ki tsaya"

Cikin dakiya ta kalleshi tace "wacece Janan?Malam ka bani guri in wuce"

"Karki raina min hankali Janan kina son kice bazan iya gane ki bane?"

Wasu zafafan hawaye suka fito daga idonta ta sake juyawa zata tafi ya rik'o hijabinta "karki min haka Janan na san kece"

Fuskarta sharkaf da hawaye tace "ba Janan bace dan Allah karka tara min mutane"

Ta fuzge hijabinta da sauri da sauri ta wuce ta cigaba da tafiya.

Shi kuma kawai yaji  zuciyarsa tayi rauni,ya sunkuya jikin motar dake kusa dashi yana hawaye an kai gab'ar da bazai iya rik'esu ba.

"Jalal kuka fa akan waccan k'azamar yarinyar?"

Ya d'ago kansa idanunnan sunyi jajir yace "waccan da kake gani ada bazaka nuna mata komai ba,kaidai kaji tsoron rayuwa kawai abokina"

"To ai naga kana mata magana tana wani zuk'ewa"

"Muyi sauri muje karta b'acewa ganina"

Yayi sauri ya tafi ya bud'e mota zai shiga Abbas yayi saurin cewa,mu had'u a gida kawai danni ban gama siyayya ba"

"Okay ga key"

"A'a zan kira sai a kawomin motana"

"No amshi kawai sai ka taho da kayan duka" yayi sauri saka masa a pocket sannan ya wuce Abbas kuma ya koma ciki.

Yana fita ya hangota a can gefe tana share hawaye.

Da sauri ya k'arasa gurin,tana ganinsa ta k'ara rikicewa tana neman hanyar da zata bi.

Hannunsa biyu ya had'e ya tsaya gabanta yace "dan Allah karki min haka Janan,babu irin neman da ban miki ba lokacin da naji labarinki raina ya b'aci saboda su Raihan basu fad'a min da wuri ba"

Kallonshi tayi har zatayi magana sai kuma ta fasa,gefenshi tabi ta wuce kawai taji ya rik'e hannunta cikin zafin rai ta d'aga d'ayan hannun ta saukeshi a fuskarsa.

"Janan" ya sake furtawa cike da mamaki.

Itama ta tsorata sosai da abinda ta aikata dan ta kasa kauda idon nata akan hannunta.

Ganin mutane sun fara taruwa suna tambayar ko lafiya ya saka ta sakin wani kukan a fili.

Kallon wani mutum tayi tana kuka tace "Malam kayi min tsakani dashi dan Allah tun d'azu yake bina yana cewa ya sanni ni ban san shi ba,kuma ni matar aurece taya zai rik'a bina? akan me?tun da nace ban sanshi ba meyasa bazai k'yakeni ba"

Ai kuwa aka yi kansa caaa ana ta fad'a masa maganganu amma ya kasa cewa komai  har lokacin hannunsa na kan kuncinsa.

Ita kanta sai take jin zafin yadda mutane suke aibunta Jalal.

DIREBAN GIDANMU COMPLETE✅Where stories live. Discover now