Page 6

356 13 1
                                    

🍁🍁🍁
   *DIREBAN GIDANMU*
        🍁🍁🍁

_*by SaNaz deeyah*_

'''Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv'''

06

Sanye take cikin doguwar riga ta atamfa,tayi rolling ta d'an k'aramin veil,idanunta d'auke da farin glass  hannunta rik'e da wani d'an k'aramin novel.

A tak'aice tayi kyau matuk'a.
Tun daya hangota ransa ya b'aci,a zuciyarsa ya furta

_wannan kyawun naki nan bada dad'ewa ba zai zama muni sai nayi watsi da duk wani farin cikin zuri'arku_

smiling yayi itama ta mayar masa dan yanzu idan ta ganshi ji take tamkar an tsundumata a aljanna"

Tana k'arasawa gabansa ta saki murmushi wanda har ya bayyana hak'oranta.

"Barka da zuwa sarauniyar kyawawa"

Wani farin ciki ne ya mamaye zuciyarta ta bud'e baki zatayi magana taji muryar Fauzah a bayansu.

"Ku tsaya ku saukeni a skul"
Duk Kansu suka jiyo suka kalleta.

A hankali ta k'arasa jikinta sanye da wata fitted gown nylon wadda tabi jikinta.

Janan kawai kallonta take rai a b'ace.

Bata sake masu magana ba kawai ta bud'e  seat d'in gaba ta zauna.

Janan ta bud'e k'ofar baya ta shiga ta zauna.

Yana driving a nutse yayinda duk kanninsu suke latsa wayarsu.

"Kayi kyau sosai Aliyu" kamar daga sama sukaji maganar.

Duk kansu suka kalleta,ta maze tamkar bata ma San sunayi ba,ta sake fad'in "ko dan dama ai kai kyakkyawane"

Shiru yayi baice komai ba,Janan ji tayi zuciyarta na tafasa tamkar an watsa mata garwashi a ciki.

"Malam kayi sauri ka saukeni karna makara"
Shi kanshi yayi mamakin yadda ta masa magana a tsawace.

Nan ma bai tanka ba ya san ranta ne ya b'aci saboda furucin Fauzah.

Suna zuwa bakin gate tace ya tsaya.
A fusace ta sauka ranta a b'ace.

       ***********

Ya kirata yafi a k'irga batayi picking wayarshi ba,da ta gaji ma kawai ta kashe wayar.

"Waye haka ya dameki har kike kashe Waya?"

"Aliyu ne bayan ya b'atan rai kuma yake kirana komai zai ce min oho"

"Aliyu kuma,wanne kenan?"
"Wanne kika Sani?"

"Ni ban san kina da wani Aliyu ba bayan direbanki"

"To shi nake nufi"
"Ta fad'a tana kallon gefe da ban"

"Karfa maganar lubna ta zama gaskiya"
"Tama zama"
"Kamarya?"
"Kamar yadda nake soyayya dashi har muna shirin yin aure"
"Direbanki"
"Ya isa haka Raihan karki saka raina ya b'aci"
"Haba Janan wlh nayi tunanin duk wasa kike amma ina ke ina direba"

"Mu tsaya a nan dan wlh raina ya gama b'aci,na kawo Salman ance baya da asali shi kuma Aliyu ai kinsan asalinsa ko?"

Jakarta ta d'auka ta bar gurin,Raihan ta bita da kallon mamaki.

Tafiya take gaba d'aya ranta a b'ace ta nutsa sosai cikin makarantar inda take ma ba mutane sosai hanyar clinic ne,kawai taji ta gabza karo da mutum,wasu stars ta gani na azaba,ta d'ago dan ta bawa mutumin hak'uri kawai taji ruwan mari har uku kafin ma ta shaida ko waye.

Ta dad'e idonta rufe kafin ta bud'e shi ta dirar dashi kan kyakykyawan saurayin.

"Hannu ta d'aga zata rama taji an rik'e ta tare da hankad'ar da ita k'asa,dariya suka hau yi sauran samari uku"

Shi kuma ya d'urk'usa k'asa saitin fuskarta yace "Janan Hashim,yarinya mara kunya,duk rashin kunyarki baza kiyi dani ba ko kuwa baki tab'a sanin waye ni a cikin polytechnic?kije ki tambaya waye yarima"
Mik'ewa yayi tsaye yana murmushi yace "kije ki tambayi ko waye ni bani da wasa musamman da talaka kamarki"

Gaba d'aya sauran mazan suka saka dariya.
"Guys muje" sun fara tafiya tayi saurin cewa "idan ka isa kai namiji ne ka fad'a min cikakken sunanka"

Juyowa yayi yana dariya ya girgiza kai kawai ya wuce.

Tashi tayi tana kad'ai kayanta sai a lokacin taji wasu zafafan hawaye na fita a idanunta.

          **********

Tana kwance tana juyi gaba d'aya hankalinta a tashe yake,ga abinda ya faru a makaranta ga  rashin sanin tak'a mai-mai inda Aliyu ya tafi domin Mameey tace tunda ya fita kaita makaranta bai dawo ba,ta kira numbershi yafi sau ashirin bai d'aga ba tana tunanin ko ramuwa yayi,bata yi tunanin kiran Fauzah ba dan bata kawo suna tare ba.

Haka ta zauna cikin k'unci ga rashin sanin sunan wannan guy d'in wanda ya wulak'anta ta a skul.


A b'angaren Ali direba kuwa bayan ya dire Janan a skul ya juya zai yi hanyar skul d'in su Fauziyya tayi saurin dakatar dashi.
"A'a Aliyu Najman hotel zaka kaini"

Yayi saurin juyowa ya kalle ta,tayi saurin zuge jakarta ta fiddo sark'ok'in gwal dasu bangles tace zan Kaiwa wata mata kayan saidawa ne,tazo daga lagos so anan hotel d'in ta sauna"

Kai tsaye ya nufi wannan katafaren hotel d'in.

Bayan yayi parking ta kalleshi ta marairaice tace "please Aliyu ka rakani bani son a min kallon banza dan Allah ka rakani muje mu fito"

"Amma idan muka shiga tare ai shine za'a miki wannan kallon"

"A'a please ni dai tsoro nake saboda ban tab'a shiga hotel ba"

"Ba damuwa muje" ya kashe motar ya bita.

Kai tsaye yaga tana tafiya ba tare data kira wayar kowa ba koda matar da tace tazo gurinta.

Sun hau bene kusan hawa uku kafin su isa d'akin kasancewar hotel d'in babba ne.

Ganin ta fito da key daga Jakarta yasa abin yayi matuk'ar bashi mamaki.

"Kika ce gurin wata kika zo naga kina k'ok'arin bud'e d'akin da kanki
" taje ta dawo shine ta bada key a kaimin"

Murmushi kawai yayi dan ya san k'arya take.

Suna shiga d'akin kuwa ta rufe da key,cire mayafinta tayi sannan ta cire bands da d'ankunnenta ta baza gashinta ta fad'a kan gado"

Murmushi tayi ta kalleshi "na mallaka maka duk kanin kaina kayi yadda kaga dama dani"

"Subhanalla kin san kuwa me kike fad'a"

"K'warai ma kuwa domin son ka ya rufe min ido"

"Wannan ba so bane"
"Wannan kuwa shine so" ta fad'a tare ta tashi zaune.

"Kaji tausayina Aliyu nayi maka alk'awarin babu wanda zaiji sirrinnan zamu rik'a zuwa nan muna biyawa junanmu buk'ata batare da kowa ya sani ba"

"Bazan iya ba,bazan tab'a aikata zina ba"

"Nima ban tab'a ba sai yanzu nake son farawa saboda na kasa b'oye feelings d'ina"

"Tunda kin san haka ai sai kiyi aure gudun fad'awa halaka"

"Abba bazai mana aure ba sai lokacin da ko wacce a cikinmu ta kammala masters ta fara aiki"

"Sai ki fad'a masa ke bazaki iya ba"

Duro wa tayi daga kan gadon ta k'araso gabansa ido cikin ido tace "kasan halin Abba yana da tsauri,Janan data fara soyayya haka ya rabasu yace shi ba zai bawa mai k'aramin k'arfi auren 'yar shi ba,sannan uwa uba baya da asali daga shi sai mamansa suke rayuwa a garin,tun lokacin daya rabamu ya hanamu kula kowa har sai mun gama masters sannan zai zab'a mana mijin daya dace damu"

"Baki da hujja,ki bud'e min k'ofa na fita"

"Aliyu pls"
"Ki bud'e nace" ya fad'a a tsawace."

_Sadeey S Adam_✍

DIREBAN GIDANMU COMPLETE✅Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon