46-47

250 7 0
                                    

🍁🍁🍁
     *DIREBAN GIDANMU*
        🍁🍁🍁

_*by SaNaz deeyah*_👄

'''Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv'''


46

Ta kirashi kusan sau goma amma yak'i d'agawa.

Ta kasa nutsuwa dan haka ta ari wayar Fauzah ta kira still bai d'auka ba.

Kuka tayi-tayi dan shi kad'ai ne jindad'inta.

Ana kiran sallar magriba suka sauka a napep ita da Fauzah, Fauzah ta biya mai napep kud'in sannan suka shiga gida.

Mameey taga damuwa a fuskarsu amma ta kauda kai kawai tace "Ku d'auki buta kuyi alwallah"

Bayan sun idar Janan ta rab'e jikin Mameey tana kuka tana basu labarin abinda ya faru tsakaninsu da Jalal.

"Gaskiya ban tab'a ganin mutum mai mutumci kamar Jalal ba yanzu da zamu rabu ya bani 50k yace inja jari kafin wani lokacin da k'yar ma na karb'a" Fahad yayi maganar

Mameey tace "ga kuma uban kayan abinci daya kawo kuma sannan yanzu yace furniture"

"Haka yace" shine abinda Janan ta fad'a tana goge hawayen da basu daina zubowa ba"

"Na yarda banyi adalci ba Mameey na zama butulu" ta k'ara fashewa da kuka Mameey na ta rarrashinta.

"Janan kin riga kin yi kuskure sai dai ki gyara nan gaba, Allah yasa ki cinye jarabawarki"

"Ameen duk suka amsa.

Bata bud'e trolley ba sai da safe bayan tayi wanka.

Wani d'an box ne baifi tafin hannu ba,tana bud'ewa taga 'yar k'aramar ring,ta d'akko ta kalla sosai taga irin English ring d'innan ce.

Wasu zafafan hawaye suka sauka a fuskarta a take ta d'auka ta zura a hannunta.

Ta janyo trolley da yace na Abba k'arami ne ta bud'a taga kayan sawa ne sababbi da kayan wasa da kuma chocolate kala-kala.

" Allah sarki Jalal wallahi ban tab'a dana sanin abinda na aikata ba sai yanzu,ina neman yafiya a gareka Jalal".

Haka ta hak'ura ta cigaba da addu'a.

Kwana biyar da zuwan Jalal Adnan ma yazo,a ranar yake sanar da ita Jalal ya tafi kwananshi d'aya har lokacin ma bai isa Singapore d'in ba.

Zuciyarsa sosai ta rik'a bugawa tayi k'ok'ari sosai wajen b'oye damuwarta  da fad'in "amma meyasa Jalal ya tafi?"

"Ya cewa Mommy transfer aka yi masa amma tace dole ya rik'a ziyartarta akai-akai"

"Allah sarki to Allah ya taimaka"

"Ameen"

Sosai suka yi hira harta manta da wani babin Jalal.

Adnan ya sanar mata ranar asabar mutumin nan zaizo kano tayi murna sosai dan gani take burinta ya kusa cika.

Sai kuma da dare da tazo kwanciya bacci ta kasa tunanin Jalal ya hanata sakat.

Tashi tayi ta d'oro alwallah ta fara jera nafiloli na neman tsari daga shaid'an dake ta mata wasi-wasi.

Mameey ma tashi tayi ta d'oro alwallah itama ta fara yi kamar yadda ta saba,sai da suka yi sallar asuba sannan suka koma bacci.

            *******

Sai da ta d'aga trolleyn sosai sannan ta dara ta da k'asa a farfajiyar gidan.

"Oyaa abar min gidan miji"

DIREBAN GIDANMU COMPLETE✅Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon