52-53

232 10 1
                                    

🍁🍁🍁
      *DIREBAN GIDANMU*
           🍁🍁🍁
        

_*by SaNaz deeyah*_👄

'''Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv'''

_Wannan shafin sadaukarwa ne gareki sister Ramlat,tnx 4 d luv & support😍._


52

Har su Mammy da Fauzah suka juya ba'a fito da Adnan ba.

Sun tafi ne da niyyar washe gari su dawo.

Sai gab da sallar isha'i sannan suka suma ganinsa.

Suma Janan tayi lokacin da ta ganshi dan ta tsorata ainun,guri kad'an ne a jikinshi ba bandeji da fulasta.

Kuka sosai take lokacin da ta tsinci kanta a kwance a gadon asibiti.

Tashi tayi da sauri ta koma d'akin Adnan d'in lokacin Mommy waya take Adam na rik'e da hannunsa.

"Sannu Janan" shine abinda ta fad'a bayan ta ajje wayar.

Janyota tayi jikinta tana rarrashi tare da cewa "ba kuka zakiyi ba addu'a zakiyi kinji".

Kai ta d'aga alamar to.

"Ga Jalal ma hankalinsa ya tashi sosai yace a satin nan zai samu yazo"

"Wlh kuwa Adam nima na ce masa yayi zamansa tunda koda yazo d'inma dubiya ce kawai amma yace a'a"

"Dole sai yazo d'in Mommy ai bazai iya hak'uri ba dan koni bazan ce karya zo ba"

"Allah ya kawo shi lafiya"

"Ameen"

Mommy babu yacce batayi ba akan Janan su tafi gida amma tace ita babu inda zataje ita zatayi jinyarshi.

Haka Mommy ta hak'ura suka tafi aka bar Janan d'in ita kad'ai.

Hannunsa ta rik'e sosai tana kuka.

Daga dare zuwa safiya nurses sunzo dubashi yafi a k'irga.

'K'arfe biyu ta tashi ta fara nafiloli na nemawa mijinta lafiya wajen ubangiji.

Da asuba kuwa yanayin sallah ta shiga toilet d'in tayi wanka saboda mutane zasu fara zuwa da gari yayi haske.

Mai kawai ta shafa a jikinta ta fesa turare,ko kwalli bata saka ba idanunma duk sun kumbura.

Material ta saka doguwar Riga mara nauyi sannan ta ajje gyakenta a gefe ta kalli inda Adnan yake kwance kamar gawa.

Komawa tayi ta kulle k'ofar d'akin da key sannan ta dawo tayi masa bed bath.

Ta gama sannan ta shafa masa turaruka ta zura masa kaya cikin dubara da k'ok'ari da jajircewa takeyin komai.

Tsura masa ido tayi bayan ta gama shiryashi,ta goge kwallar idonta tace "kaman ba kai ba Adnan lokaci guda kamaninka sun canza"

Ta zauna kan kujera tare da rik'o hannunsa tace "karka mutu dan Allah Adnan,ina buk'atarka a raye saboda mu cika burinmu na rayuwa ina son ka dan Allah ka tashi"

Sunkuyar da kai tayi ta cigaba da kuka a wannan kukan bacci ya d'auketa.

Ji tayi an d'an bubbugi kafad'arta,ta bud'e ido a hankali ta kalli nurse d'in.

"Bacci kika samu?"
Murmushi tayi tare da cewa "ban ma san ya d'aukeni ba"

"Kiyi hak'uri sister Addu'a zaki cigaba da yi kinji,duk da dai munji ance jiya aka d'aura auren ku lallai dole ki shiga tashin hankali amma dai addu'a itace magani"

Kai kawai ta d'aga.

"Ga wannan k'arfe takwas likita zaizo za'aje lab a k'arbo jini sannan za'ayi test da yamma"

DIREBAN GIDANMU COMPLETE✅Where stories live. Discover now