48-49

315 12 6
                                    

🍁🍁🍁
     *DIREBAN GIDANMU*
          🍁🍁🍁

_*by SaNaz deeyah*_👄

'''Dedicated 2 Miss Xerks &  Safnah luv'''

_~kowa ma ya san ke tawa ce,wollah ko bakiyi na ni ina yinki sosai my Aunty😘~_


*_Zuwa ga makaranta wannan littafin,naji k'orafe k'orafenku amma ina mai tabbatar muku cewa har na gama novel d'in nan bazanyi abinda bazai gamsar daku ba,karku duba dad'in novel d'in nan sosai kawai ku duba fad'akarwarsa,na tabbatar abubuwan da suke faruwa a yanzu akwaisu a littafin nan kuma in har akwai abinda ya zama akasin haka ko kuma kuna ganin babu fad'akarwa dan Allah ina son comments ya isa gareni kai tsaye babu wani b'oye-b'oye._*

48

Kanta na cikin gwiwarta har lokacin da Fahad ya gama basu labarin rasuwar Ummi abinda ya faru, amma Janan bata d'ago kai ba.

"Wannan fa meya sameta?"

"Ita da Fauziyya ne"

Kallon Fauziyya yayi yace "me kika ma autarmu mun samota da k'yar kina neman b'ata mata rai"

"Yaya nifa wasa nake mata,amma wallahi ka jawa autar nan kunne bata jin magana taurin kai ne da ita har yanzu"

"Ai a gurinki ta koya"

Ya dafa kan Janan yace "kiyi hak'uri Janan ki rabu da ita kinji"

Kai kawai ta gyad'a daidai lokacin wayarta ta fara ringing.

'Dan juyar da kai tayi sannan ta goge hawayen idonta ta d'aga wayar.

"Salamu alaikum"

Daga d'ayan b'angaren Momma ta amsa da "wa alaiki salam Janan ya kike ya gida?"

"Lafiya k'alau Momma ya su Zainab da Humaira"

"Zainab k'alau suke suna gaidaki,wato kinga mama shine kika guji Momma ko?"

Murmushi tayi tamkar Momma na gabanta tace "a'a ai zan koma insha Allahu"

"Ai tace da kanta zata zo ta d'auke ki jibi"

"To Momma"

"Kina wace unguwa a kano?"

"Kuntau ne daidai layin makaranta"

"Okay muna nan tafe yau d'in nan"

"Yau Momma, eh mana ai tun jiya muna Abuja yanzu mun taho kano ni da Muhasin"

"To Allah ya kawo ku lafiya"

"Ameen Janan ki gaida mamanki kafin mu k'araso"

"To"

Katse wayar tai batayi niyyar fad'awa su Mameey ba saboda yadda ranta ke a b'ace.

Amma da Mameey ta tambayeta kawai sai ta fad'a.

Babu shiri suka d'aura girki,Fahad ne ya fita ya sayo k'ank'ara Fauziyya ta had'a zob'o mai dad'i.

Duk abinnan da ake har lokacin bata saki ranta ba.

Duk da suna cikin aikin Fauziyya ta bata hak'uri tare da cewa haushi taji shiyasa tayi furucin.

Ita kuwa ta kudurta a ranta babu wanda zai hanata komawa gidan Aliyu ko dan ta hukuntashi akan abinda ya masu.

Kusan k'arfe hud'u su Momma suka k'araso.

Hankalinta sosai ya tashi ganin Abba k'arami a hannun Muhasin tamkar gawa.

Da sauri ta kai hannu zata karb'eshi suka had'a ido da Mameey ta fasa.

Iso aka masu bayan sun gaisa Momma ta kalli Janan wadda damuwarta ta fito k'arara.

DIREBAN GIDANMU COMPLETE✅Where stories live. Discover now