36-37

297 11 1
                                    

🍁🍁🍁
      *DIREBAN GIDANMU*
     🍁🍁🍁

_*by SaNaz deeyah*_👄

'''Dedicated 2 Safnah luv & Mrs Xerks'''

_kuyi hak'uri fans_

36

A hankali ta bud'e idanunta tana k'arewa d'akin kallo.

Abubuwan da suka faru ne suka fara dawo mata tayi saurin tashi tana kiran "d'ana ina yarona?" kuka sosai take tana furta ina d'anta.

A rud'e nurses biyu suka shigo.
"Lafiya ya kike jin jikin naki?"

"Ina d'ana?" ta sake tambaya tana kuka.

'Daya daga cikin nurses d'in ta dafata tace "baiwar Allah ki kwantar da hankalinki d'anki yana cikin kulawa kinji"

"A'a Ku fad'amin inda yake inje in ganshi dan Allah"

Ganin ta rud'e ne yasa suka rakata har d'akin da  Abba k'arami yake.

A rud'e ta k'arasa jikin gadon tana k'ok'arin d'aukarta suka hanata.

"Baki ganin baya da lafiya?ki bari ya tashi sai ki d'aukeshi"

Kuka ta fara ganin fuskarshi da bandeshi,tana fad'in "karka mutu Abba k'arami dan Allah karka mutu ka barni kaine gatana ka tausaya min kaji"

Su kansu nurses d'in sai da suka tausaya mata.

Kujera taja ta zauna ta kifa kanta akan gadon ta cigaba da kukan da ta san bazata tab'a dainawa ba.

         ********

Yana jingine da filo hannunsa rik'e da kansa yana cije leb'e cikin jin zafin ciwon yace "doctor  yanzu ko da sanda bazan iya taka k'afata ba?"

Murmushi doctor yayi yace "kana cije leb'e amma kana tunanin tafiya a yanzu?"

"Indai zan iya takawa to zan tafi"

"Zuwa ina?ai in fad'a maka su Mommy suna kan hanya dan na fad'a mata komai" Abbas yayi maganar.

"Me?ka fad'awa Mommy dagaske?haba Abbas meyasa zaka min haka?"

"Saboda ina sonka kuma kasan bazan bari rayuwarka ta lalace akan wata banza ba,dubi yadda ka koma kayi wuju-wuju kusan kullum  ana abu d'aya"

"Wa'izubillah,Abbas kana daukar alhakin Janan me tayi maka?shin ka santa a baya ne ta maka laifine?akan me zaka rik'a muzantata?"

"Saboda kana da mata,na tabbatar idan Raihan taji bata tab'a jindad'i ba"

"To bari Raihan d'in tazo sai na tabbatar mata naga Janan kaji me zata ce"

Shiru yayi baice komai ba shima Jalal ya kwanta ya juya masa baya.

Da yamma su Mommy suka k'araso aikuwa ta rufe Jalal d'in da fad'a akan me yasa zai samu ciwo amma ya kasa fad'a mata.
Raihan kuwa har da kukan ta.

Adnan lallab'a shi ya rik'a yi yana masa sannu.

Sunso su mayar dashi can asibitin a Abuja amma yak'i yarda dole ta sa suka juya Raihan kuma ta zauna dan ta cigaba da kula dashi.

Bayan sallar Magrib Najwa tazo,ganin Raihan ne yasa tayi turus tana neman watso tambaya dan yadda taga Raihan na wani shishishigewa Jalal.
Abbas yayi saurin tarar numfashinta da fad'in "wannan matar Jalal ce sunan ta Raihan"

"Oh sannu" ta fad'a ranta a d'an b'ace

"Yawwa,wacece wannan Jalal?"
Tayi tambayar tare da kafeshi da idanu.

"Itace wadda ta kad'eni" ya fad'a kai tsaye
"Oh kece kika so rabani da farin cikin raina ko?" Ta fad'a tana murmushi

Ganin hakane yasa itama Najwa  tayi murmushin tace "a'a tsautsayi dai ko"

DIREBAN GIDANMU COMPLETE✅Where stories live. Discover now