Page 9

243 13 1
                                    

🍁🍁🍁
       *DIREBAN GIDANMU*
         🍁🍁🍁

_*by SaNaz deeyah*_👄

'''Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv'''


_Wannan Shafin naku ne 'yan group d'ina *TASKAR SANAZ* bazan iya musalta farin cikina a gareku yadda kuke bani k'arfin gwiwa akan novels d'ina,nagode sosai ina alfahari daku Allahu ya barmu tare ya kuma bar zumunci_
*#ILYMTYE😍😘*

09

Fridge ta bud'e ta d'akko lemo da ruwa ta d'ora kan plate d'in sannan ta d'auki cups guda biyu ta nufo inda suke ta ajje
"Bismilla"

Ruwa suka zuba suka sha sannan Ummi ta sake tambayarta Aliyu a karo na biyu.

"Nafiso sai kun ci abinci kun huta yanzu za'a kawo maku"

"Dan Allah ki fad'a mana gaskiya ko dai ya mutu ne kike son b'oye mana?" Zuhra ta tambaya.

Ajiyar zuciya tayi ta kalleta tace "ki kwantar da hankalinki Aliyu yana raye nd am vry sure lafiyarsa k'alau"

"To idan hakane yana ina?" Ummi ta tambaya.

"Kinsan ai. .........." Knocking da ake na k'ofa yasa tayi shiru tare cewa "shigo"

'Yan aikinsu suka shigo hannunsu d'auke da tray na abinci da plates sai plate d'in fruit .

"Bismillah Ku ajje" tayi masu umarni,bayan sun ajje sun fita sannan ta juyo ta kallesu.

"Ai ya fad'a maku abinda ya faru jiya ko?"

"Eh amma wallahi yaya bashi da laifi bazai tab'a iya aikata zina ba"

"Hakane nima zan shaideshi akan hakan,amma matsala d'aya da suka zauna d'aki d'aya a hotel kuma da Abba yazo sai  ya gudu,shiyasa kowa ya shiga zulumi akan shiya jata ko ita taja shi"

"Amma kinsan idan mahaifinku ya zo a lokacin yaya baya da wani uzuri zai iya fuskantar ko wace matsala"

"Toh,yanzu dai Abba yasa an tafi dashi cell tun jiya itama yaya fauziyya ya saka an kulleta a d'aki sannan yace babu belin"

"Na shiga uku ni Ummi me zan cewa umma meyasa rayuwarmu ke tafiya a haka"

Zuhra ta ruk'o Ummi tana kuka, hakan ne yasa Janan taji hawaye ya sauka a fuskarta.

"Yanzu ko ganinsa bazamu iya yi ba?" Zuhra ta tambaya.

"Za muje daku Ku ganshi"

Da sauri Ummi ta tashi ta kalli Janan "dan Allah mu tafi yanzu ki taimaka mana"

Tausayi ta bata sosai dan haka ta tashi ta d'auki mayafi sannan ta d'auki jakarta ta kallesu "zamuje mufara yiwa Mameey sallama amma dan Allah Ku goge hawayenku Ku saki ranku karta gane wane abu bare ta hanamu zuwa"

Haka suka tashi jiki a sanyaye suka fita,Mameey still tana falo,Janan ta zauna kusa da ita tace "Mameey ina son kaisu gida gashi babu direba"

"Ina Mato?"
"Kin san mato ba yawan zama yake ba,Baita kuma ya fita da Abba"

"To ya za'ayi?"
"Mameey inyi driving d'in?"
"Ina tsoron fad'an mahaifinku Janan"
"Zan dawo kafin ya dawo insha Allah"
"Okay ki kiyaye janan karki ja mana fad'a"
"Insha Allahu"
"Kije d'akina ki d'akko masu laces guda biyu da turaruka,ki basu 10k"
"To Mameey"

"Mun gode Allah ya saka da alkhairi" Zuhra ta fad'a.

Ummi kuwa ba yabo ba fallasa.

Da sauri Janan ta shiga d'akin mameey ta d'akko komai kamar yadda ta fad'a.

DIREBAN GIDANMU COMPLETE✅Where stories live. Discover now