Page 54-55

324 9 2
                                    

🍁🍁🍁
     *DIREBAN GIDANMU*
          🍁🍁🍁

_*by SaNaz deeyah*_👄

'''Dedicated 2 Miss Xerks & Safnah luv'''

54

Ya kasa zama guri  d'aya ya zauna ya tashi duk abin duniya ya ishesa.

"Mommy meyasa zaki hanani yin abin alkhairi?"

Dafe kai yayi yana tunanin mafita.

Can yayi murmushi ya d'auki wayarsa yayi dialing number Saifuddeen ringing d'aya ya d'aga.

Gaisawa suka yi tare da jajen kwana biyu basu had'u ba.

Babu wani jinkira ya bashi labarin komai.

Daga d'ayan b'angaren Saifuddeen yayi murmushi yace "haba kai kuwa meye na d'aga hankalinka bayan akwai iyayen bogi kawai su za'a biya suje"

"Amma Saif kasan babu wanda baisan Mahaifina ba"

"Kuma babu wanda bai san ya rasu ba kawai ka sakasu a matsayin uncles d'in ka ne"

"To kana ganin har nawa za'a basu?"

"Bari yanzu zan fita idan na nemosu aka yi ciniki sai na kira ka ka tura ta account kaga goben sai muzo Abuja tare dan nima jiya na dawo Kaduna"

"Okay ba matsala nagode"

Katse wayar yayi ya zauna gefen gado tare da dafe kai a zuciyar sa yace _Amma nayiwa Mommy adalci kuwa?ta hanani yin abu nayi,ko dan na san Mommy nada fahimta idan komai ya lafa suka dawo da Amal daga can muma lokacin mun dawo daga Egypt na san Mommy baza tace komai ba dan tana da hak'uri._

_Janan fa shin ka mata adalci wulak'ancin da kai mata d'azu?_ wata zuciyar ta sake hangod'o masa question.

Ajiyar zuciya yayi a fili yace "gaskiya ban kyauta amma itama ai bai kamata tamin wannan furucin ba"

Wani irin ba dad'i yaji jikinsa a sanyaye ya tashi ya figi motarsa zuwa asibitin.

         **********

Kallonta tayi rai a b'ace tace "dalla malama in zaki saki ranki ki saki haba Najwa kefa ba yarinya bace,shikenan d'an abu k'ank'ani ya d'aga miki hankali"

Kallonta Najwa tayi tace "lallai Preety kece kike ganin abin kamar wasa amma banga laifinki ba tunda baki san zafin so ba"

Dariya sosai Saudat tayi tace "ina zansan zafin so tunda ban d'orawa kaina wahala ba,ni samarin ma wasi nake dasu in naga dama"

"Ke kika d'auki so a matsayin wahala saboda ke baki san so ba baki tab'a yin soyayya ba"

"Kina nufin duk tarin samarin da nake dasu ba sonsu nake ba kuma suma basa sona?"

"Ba haka nake nufi ba ina nufin har yanzu ke da samarin naki wasa kuke ko kuma yaudarar juna,so d'aya ne kuma Jalal nakewa nawa idan har bazaki taimaka min ba to ki daina rab'ata"

Dafata tayi tace "me yayi zagi haka,kiyi hak'uri k'awata kinsan wannan shine abinda ya kawo ni gidannan saboda Mommy tace ta kasa gane kanki kullum cikin damuwa kike kin daina ko fitowa falo kuma tasan baki da wata aminiya da ta wuce ni"

Uhmm "Saudat ina cikin mawuyacin hali wallahi so na neman haukata ni ina zanga Jalal,Jalal ya gujeni Saudat numbers d'insa sun daina shiga sau biyu ina zuwa gidan su Abbas baya nan na rasa mafita"

"Gidan su Abbas meye zakije gidan su Abbas kuma?"

"Abbas ne abokinsa dan ko lokacin da yazo garinnan a gidansu ya zauna zan tambaya da ya bani new number Jalal"

DIREBAN GIDANMU COMPLETE✅Where stories live. Discover now