Page 2

308 21 0
                                    

KOWA YA GA ZABUWA...
(DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

*PAGE 2*

*FREE BOOK*

"Maman Usman yaron nan ai ba chemist ya kamata ki kawo shi ba asibiti ya kamata ki kaishi yana jin jiki sossai.."
Share hawayen ta tayi sbd mammatsa cikin Usman da malam Musa ke yi yana ƙara cikin azaba se taji ina ma zata iya cire mishi ciwon ya dawo jikinta Allah sarki uwa kenan.

Cikin damuwa tace
"babu halin ne Dr da akwai da na kaishi, in na tafi asibiti da dubu guda babu me saurara ta, ka taimaka ka bashi ko na rage zafi ne kan in je in nema Dan Allah"
cike da tausayinsu Dr Musa ya Haɗa musu magani kuma be karɓi kuɗin ba yace
"ku je ku gwada Allah ya bashi lafiya"

Ta mika mishi kuɗin
"gashi se ka cire"

"A'a maman Usman ke de Allah ya bashi lafiya"
Godiya sossai tayi mishi kan ta kamashi Aisha ta taya ta suka dawo gida, ruwa ta samu ta bashi ya sha ya kwanta bacci ya samu ya ɗauke shi.

Zugum ta zauna tana Tunanin yadda zata bi da dubu gudan nan har ya kai musu karshen wata, kaman yadda Hamma Yusuf ya faɗa ko da mutuwa take idan har watan nan be kare ba ba basu kuɗin nan ze yi ba, dafata da Aisha tayi yasa ta buɗe idanunta da suka yi laushi da gajiya, yunwa, damuwa da ciwo ta zube su kan yarinyar.

"Mama Tunanin me kike?"

Aisha na da wayo ko ta ƙi faɗa mata haka zata yi ta naci tayi ta naci se ta sani.

"Ina Tunanin yadda kuɗin nan ze kaimu wata ne Aisha"
Ta faɗa mata ne kawai ba don wai da tunanin samun mafita daga yarinyar ba, ita ma rashin abun cewa ya sa tayi shiru kawai ta zubawa wuri guda ido..

Kaman saukar aradu haka taji a sadda kunnuwanta suka jiyo mata sallamar wasu mata da suka shigo su hudu, akallah ba akasara ba babu wacce zata haura 28 cikinsu, se matashiya da zatayi sa'a da Hidayat kaman yadda naji Hamma Yusuf ya faɗa sunan.

A maimakon farin cikin da kowa yake yi idan yayi baƙi saɓanin Hidayat tashin hankali ne ya bayyana karara a fuskanta tana shirin magana ɗaya daga cikinsu tace
"Shafaffiya da mai yau ko arzikin sannu da zuwan ba zamu samu ba kenan ana baƙin ciki da lafiyarmu"

Baƙar tace
"Eh to Salamatu ba dole tayi baƙin ciki da lafiyanmu ba tunda da shine muka tako muka zo har gidanta"

Matashiyar tace
"A'a Aunty kausi gidan ɗan uwan mu dae... Ni wlh in banda ya Yusuf banga abun ɗauka a wanna ƙashi da ran ba se fari kaman aljana"

Na karshen tace
"ke kuwa Surayya baki da labarin ita ce ta shiga ta fita sbd ta sha a nono tayi yadda tayi ta sa shi Yusuf ɗin ya fara son ta har Abba ya Haɗa auren, to da aka zo ba'a samu yadda ake so ba kuma an kasa bari an manne kaman dangin maita"

Na farko wacce aka kira Salamatu tace
"To wa ya sani Abu a duhu.."

Budurwar Surayya tace
"a kuma cikin baƙar Leda"

Suka kwashe da dariya...

Aunty kausi tace
"wai kuma dan bala'i Da aka tashi auren aka Haɗa da nawa Abba har da yiwa wannan munafukar annamimiya kayan da suka fi nawa har yau in na tuna kaman in mutu"

Dariya duk suka yi Salamatu tace
"ki bar ɓata ranki yanzu duk suna ina?"

"Gidan Boka"
Cewar Fahariyya itace ta karshen.. Suka kwashe da dariya tare da tafawa..

KOWA YA GA ZABUWA...Where stories live. Discover now