Page 17

250 18 0
                                    

KOWA YA GA ZABUWA...
   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            
         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

                      *PAGE 17*

*FREE BOOK*

"Ya Hamza..!"
Ta faɗa tana wara dukkan idanunta da ta saka musu kwalli waje, duk da yadda ya kara girma da jiki ya tara kasumba gwanin burgewa hakan be hanata shaida shi ba a kallo ɗaya sbd shine mutum na farko da ya fara nuna mata ƙauna a duniya bayan Abba kuma kullum yana ranta..

Shi kuwa kokarin ce mata sorry yake amma ganin ta kira sunanshi yasa ya ɗan dakata tare da sanya mata idanu na seconds se kuma ya waro su gabaɗaya yace
"Hidayat!"

Dariya suka saki a tare yace
"what a coincidence! Hidayat me kike yi a Paris? Taya kika zo?"

Tana murmushi tace
"labari ne mai tsawo"

Yace
"then mu je mu zauna se in ji da kyau, aurenki fa?"

Kanta ta ɗan dukar tace
"ya mutu"

Wani sihirtaccen murmushi ya saki tare da Juyawa ta bi bayanshi Sam ta mance ma da Aisha jiran ta take da ice cream ɗin da ya ɓare again, wurin wasu kujeru guda biyu suka je suka zauna yana tsokanarta akan ta ƙara girma tayi kyau tana ta dariya..

Daga inda yake zaune sanye da designers Riga da wando na kamfanin Versace idanunshi sanye da designer shade na Swarovski ba karamin kyau yayi ba barin ma sabon diamond ear ring da ya sauya dake ta kyalli, tun da ta mike ya tsinci idanunshi a kanta har ta shige be dauke ba, daidai fitowanta da karon da suka yi duk a kan idanunshi..

Ganin suna dariya da magana alamu sun san juna yasa ya ɗauke kai yana jan tsiririn tsaki, agogonshi ya kalla se ya ɗauke kai again, Aisha dake zaune ya sake kallo ya ɗaga kai ya kalli sun nemi wuri sun zauna suna ci gaba da dariya, wani irin ɓacin rai ne ya bijiro mishi da be san na menene ba, miƙewa yayi kaman ze nufi inda suke se ya fasa ya shiga shagon ya sayo wani ice cream ɗin ya zo ya ba Aisha duk yana kokarin hana idanunshi kallon ɓarayin da suke..

Ita kuwa Shap ta ma mance dasu, a hankali take ba Hamza labarin abubuwan da suka faru tun tana dauriya har ta fara kuka tana zuwa wurin rasuwar Abba ta dakata tana hawaye sossai, handkerchief hamza ya ciro ya mika mata ta saka hannu zata karɓa se suka Haɗa idanu..

Idanunshi sun sauya sossai wadda kallon cikinsu ya haddasa mata wani mummunar faɗuwar gaba, a table ɗin ya zo ya zube hannayenshi ya ɗan duƙa kaɗan yana kallonta ba tare da ya kalli hamza ba yace
"can u please get up mu tafi? U can't keep me waiting for u miss hidayat don't forget am ur boss"

Mikewa tayi da sauri tace
"Sorry sir..!"

Tsaki ya ja ba tare da ya kalli inda Hamza yake ba ya juya ya wuce.

Hamza yace
"who is he?"

A sanyaye tace
"my boss as he says, bari na tafi we continue in muka haɗu gobe"

Yace
"ur digits pls"

Ta karɓi phone nashi ta saka mishi tana kallon motan Raed da har ya tayar, da sauri ta karasa ta buɗe baya ta shiga bata gama rufe motar ba ya fisga da gudu ya bar wurin..

Har suka isa gida yana cin rai ko yaran babu wadda ya cewa kala, Kimorah da ya samu ce ta ɗan rage mishi damuwar da yake shirin bijiro mishi wadda ya mance ya kalar damuwar take tun da ya sa kafa ya bar gidan uban shi..

KOWA YA GA ZABUWA...Where stories live. Discover now