Page 3

284 19 0
                                    

KOWA YA GA ZABUWA...
   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            
         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

                      *PAGE 3*

*FREE BOOK*

Tunaninta ya yanke ne a sadda taji ta dafe kyauren gidan tana sauke ajiyar zuciya da godiya ga Allah da be bari ta kai ƙasa ba, da kallo ta bi budurwar da ko waiwaye bata yi ba har ta shige sashen Yusuf, girgiza kai tayi duk cikin ƴan matanshi da yake kawowa gidan babu marar mutunci kaman firdous, in har ta zo ta dinga wahala kenan.

A ganin firdaus hakan ne ze rage mata kishin Hidayat tunda Yusuf ya ki sakinta, bata da masaniyar da tana da inda zata da bazata taɓa zama da wannan kadararren auren ba.

Tsaki tayi ita tun kawo ƴan matanshi na damunta har ya zo ya dena damunta kwata kwata, ɗaki ta shige ta kishingiɗa jefi jefi su kan yi magana da Usman Aisha ta tafi islamiyya, anan ne ma ta yanke shawarar ta fara sana'ar gawayi.

"Mama in na girma bazaki sake yin wahala ba, zan gina miki babban gida da mota in zuba miki masu aiki irin na gidan Alhj mudan"

Murmushi ta saki tana kallon Usman ɗin da tsakaninsu da Aisha kwata kwata shekara ɗaya da rabi kenan don yanzu yana cikin shekara na 6 da ƴan watanni, tace
"in shaa Allahu babana, Allah ya bamu yawan rai"

Cike da jin daaɗin ganin murmushinta yace "Ameen".

Ta miƙe tana saka hijab tace
"bari in shiga nan maƙota in nemi yaron da zan aika ya saro min gawayi a chan hanyar hadeija yafi kyau"

Yace
"Mama gawayi zaki fara sayarwa?"

Tace
"eh Usman, ka ga unguwan nan babu masu sayar da shi sossai kuma ana amfani dashi, dayawa se sun je layi na gaba suke samowa kaga zamu yi ciniki in shaa Allah"

Gyaɗa kai yayi yace
"Allah yasa kar su maman zubair su hana ki, kaman yadda suka zo nan suka hana ki sayar da kayan miya"

Murmushi kawai tayi tare da girgiza kai, yaran yanzu se a hankali komai sun sani, tana tafiya tana Tunanin yadda mutanen unguwan suka haɗe mata kai sbd ɗan cinikin da take yi a kayan miyan da take sayarwa karfi da yaji suka sa ta dena sana'ar su suka cigaba se a lokacin ta san eh lallai duk kankantar samunka wani baƙin ciki yake da kai, baƙin cikinta da sana'ar take samun na biyawa yaran nan ɗan kuɗin PTA da na islamiyya se kuma ɗan abunda zasu saka bakin salati Dukda shima ba na arziki bane, suturu kam ba'a magana.

Har ta isa gidan tana Tunanin duniya, da sallama ta shiga daga tsaye suka gaisa da matar gidan da ta kira da Asabe, kan ta ɗaura da
"Dan Allah ko a cikin yaran akwai wadda ke kusa aike ne nake ɗan so in yi"

Habiba dake kofan ɗakinta tayi Charab tace
"se kuma ki rasa yaran aike se na gidan nan?"

Bata kalleta ba idanunta na kan Asabe da Seda ta jira karshen maganan habiba kan tace
"kin ga kuwa wlh duk basa nan kiyi hakuri in sun dawo ko zuwa gobe se in turomiki ɗaya daga cikinsu"

Lantana dake zaune kofar ta tana tankaɗe tace
"munafunci da iyayin banza, in an ga dama a karɓa kawai a je yanzu ba se an jira yara ba karshen soyayya da tausayi kenan"

Habiba da Zulai da itama ta ɗaga labule tana jin Abunda suke faɗa suka kwashe da dariya.

Fita Hidayat kawai tayi ba tare da tace musu komai ba, bata san me ta tare musu ba ita rayuwar da take ciki ma kaɗai ya ishe ta, yadda suke mata ko tsakaninsu da suka Haɗa miji basa yi se da ita.

KOWA YA GA ZABUWA...Where stories live. Discover now