Page 41

293 22 0
                                    

KOWA YA GA ZABUWA...
   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            
         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

FOLLOW ME ON Wattpad @Gureenjoh6763

AND ON AREWA BOOKS @gureenjo

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

                      *PAGE 41*

*FREE BOOK*

*Sorry! Jiya bamu da wuta wayana ya mutu kan wuta ya dawo kuma na wuce Garinmu a bacci! Yauwa I want to talk about ghost readers, kun ganku? Babu na gode, babu comments se an kwana biyu ba'a ganka ba se kaga ana cewa "wacce kam shiru!" "Yau babu kowa yaga zabuwa" ko kuma masu cewa "continue" Abeg ku duba wahalar da mutum yake sha wurin wasa kwakwalwa, data, hannu da idanu wurin faranta muku ku faranta mishi kuma... Typing is not a joke I repeat ba wasa bane wlh! Allah yasa mu dace***

Wuta sossai ya tashi a gidan ba tare da na sani ba saboda baccina ba na lafiya ba, wata ce ta zo ta tada ni karfi da yaji ta Jani muka hau gudu muka fita daga gidan kaman yadda sauran jama'ar gidan kowa yayi ta kanshi yayinda wasu daga ciki suka ƙone kurmus ciki harda magajiya, dab asuba kowa ya kama gabanshi haka nima na nausa nayi ta tafiya ban damu da dubun dare ba banda jakana da nake rungume dashi ba dare ba rana ko takalmi babu kafafuna.

Karnuka sede su min haushi su gaji su wuce amma ko ta kansu bana bi bare in tuna wani abu wai shi tsoro, jikin wani gida na samu na zube a wurin saboda gajiya da nayi ga bacci ina ji, pillow nayi da jakana na hau bacci a wurin Dukda uban sauro dake yawo a unguwar.

"Baiwar Allah! Baiwar Allah!!"
Wata murya ke ta ambaton hakan har Seda na fara buɗe idanuna ina lumshewa, ganin garin yayi shaaaa Dukda be zama haske tangararam ba hakan yasa nake iya kallon kamilalliyar fuskanshi yace.

"Me kike yi anan haka da tsohon ciki? Na fita zan je masallaci na ganki har kuma na dawo baki tashi ba! Baki tsoron sauro ya illatar dake da abunda ke cikinki?"
Ban amsa ba se Kallonshi kawai da nake, chan na iya buɗe baki kaman an fusgo maganan nace
"ru....wa"

Yace
"tashi! Tashi mu shiga gida se in baki kisha"

Da kyar na iya mikewa sbd nauyin jiki da ciwon kafafu, haka muka shiga gidan nashi tun fitowa ta shine mutum na farko da ya tausayamin har ya taimake ni ba tare da ya san ko ni wacece ko daga ina nake ba!

Mutum ne me matsakaicin karfi don baza'a kirashi me kuɗi ba, gida ne daidai na rufin asiri, sallama yayi cikin babban sashen.

Wata mata ta fito tana kallonmu ɗaya bayan daya, yace
"Umman khausar ga bakuwa nan don Allah kaita extra room ɗin nan ki bata ruwa in akwai wani abu a gidan ki bata kan a gama abin kari!"

Kallon tara saura kwata take mana daga ni har shi seda ta gama kare mana kallo kan tace
"amma Abban Yusuf ka ma raina min wayau, haka kawai ka shigo min da mace da tsohon ciki rimi rimi ka wani ce in bata extra ɗaki da abinci? Ina ka samo ta da sassafen nan?"

Yace
"tsaya tukuna Amina gidanki ne nan kam ko gidana? Taya zan ce ga abunda za kiyi kice ba haka ba matar nan tana tsaye tana jin jiki?"

Dariya tayi ta tafa hannu tace
"Aaaa lallai ni dayake ba ciki ne jikina ba a kwance nake ina jin daaɗi, taya zaka fara fifita wata kaina? Kab zuri'arku ban san me kama da aljannu ba bare in ce daga dangi take.."

Juyawa yayi ya kalleni yace
"zo mu je baiwar Allah"

Juyawa muka yi zamu bar wurin tayi wani tsalle ta sha gabanmu ko damuwa da cikinta da ya ɗan fara fitowa bata yi ba tace
"Ina Zaku je? Wai me kake nufi ne?"

KOWA YA GA ZABUWA...Where stories live. Discover now