Page 26

291 21 0
                                    

KOWA YA GA ZABUWA...
(DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

*PAGE 26*

*FREE BOOK*

Fisgota yayi da karfi kan ta ƙarasa kanta ya nuna ta da yatsa yace cikin harshen turanci
"karki kuskura ki fara abunda bazaki iya ba... Now! Get out of my house...!"

Idanunta gabaɗaya ta waro tace
"what do you mean?"

"I mean it's over between us.."

Kuka ta fashe dashi a zuciye ta wuce room da ta kwana ta janyo kayan ta ta fito ta sauka da gudu tana kuka.

Tsaki yaja yana ɗauke kai daga kallonta se suka Haɗa idanu wani irin numfashin tsoro take ta saukewa, kanta ta mayar kasa tare da cewa
"Seda safe"
Bata jira amsar shi ba ta wuce

Washegari shi ya sauke ta a makaranta Dukda dae ba wani hira suka yi ba bayan gaisuwa sede fuskanshi a sake ba kaman sadda yake fushi ba kuma sossai taji daaɗin hakan.

****

Roba me ɗauke da garin kunu kaɗan da kuma kullin tsamiya da gyaɗa ta dire mata.
"Tashi ki yi min kunu karki yarda tsamiya yayi yawa kuma ya nuna kar yayi ruwa"

Kallonta Surayya tayi zata yi magana suka Haɗa idanu da Umma ta girgiza mata kai alamun kar tayi.

Miƙewa Surayya tayi ta ɗauki robar kunun ta yi bakin murhu tana mitan..
"Kece matsiyaciya da kike shan kunu in ba da yanzu rayuwa ya chanza ba ai ko sunan kunu ba'a kira mana gida daga custard se oat"

Tak bata ce ba ta samu kujera ta zauna, a cike take da su dukkansu kuma kaɗan take jira kab ta saita musu zama, umma dake zaune cikin Asabar da Lahadi na kodaddiyar Atampha ta zabga tagumi tana Tunanin Abba

A lokacin da yayi mutuwar son tayi karatu ko don bayan ranshi tayi amfani da aikinta wurin kula dasu sede Sam ta ƙi tana ganin yana dashi ko ya mutu ba zasu yi rashi ba, ya sha gayamata dukiyar gado iska ce tsab se ta iya bin me shi cikin lokaci ƙankani, ya sha gayamata rayuwa ba tabbas sede duk tayi watsi da hakan.

Yau a yanzu wa gari ya waya? Da Kausar taƙi karatu ma ita ce ta bata goyon baya haka Abban ya hakura ita kuma fahiriyya a sadda zata auri mijinta da take aure ya shaida musu ba karatu a gidanshi Abba ya ƙi bada ita ba karamin bore suka yi ba haka ya hakura ya zuba musu idanu, ita Surayya da take ɗan karatun an kore ta saboda rashin kokari gatan da ta nuna mata na Hidayat take yi mata komai ciki har test da exams ya ja mata.

Yusuf bashi da maraba da mahaukaci, wanchan kuma bata ma san duniyar da yake ba..! Wata ashariya da hafsatu ta saki ne ya katsewa Umman tunani.

Mari ta gaure Surayya dashi tace
"don uwarki wanchan dake zaune haka na baki umarnin dama min kunu?"

Surayya tace
"Wallahi ba de uwata b..."

Kwashe ta da tayi ya hana maganan karasa fitowa, se ga Surayya a ƙasa wanwar dama gata kaman karan kaɗa miya, danne ta hafsatu tayi bata damu da zafin kunun ba ta fara ɗura mata tana cewa
"yau se nayi maganin bakin rashin kunyar nan..! Zaki san ni kika yi kokarin zagi"

Ga tsinkakken kunu, ga Shakura, ga tsami saboda tsamiyar da ta labta don mugunta ga rashin sugar da zafin kunun duka ya Haɗar mata shidewa take sede ko a jikin hafsatu, ba ta sake ta ba seda taga kunun na fitowa har ta hanci ga idanunta kaman garwashi ko da ta sake ta mikewa tayi ta fara kwara amai tana tari kaman zata mutu.

KOWA YA GA ZABUWA...Where stories live. Discover now