Page 11

239 17 0
                                    

KOWA YA GA ZABUWA...
   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            
         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

                      *PAGE 11*

*FREE BOOK*

**Ameeratuh kin hana ni baccin safe🤧 ga shinan kan ki zo min a mafarki🚶‍♀️🚶‍♀️**

"Hidayat haba mana kar imaninki yayi ƙaranci ki dinga furta kalmomin da zaki je kiyi saɓo, Usman kwanan shi ya riga ya ƙare shine dalilin mutuwar shi Sam baki yi Sila ba sbd be yi gaggawa ba mu ma kuma ba jinkiri mu kayi ba, yau kwana bakwai kenan bakya ci bakya sha, sbd kuka dubi idanunki yadda suka koma ki kalla ki ga Aisha yadda take a firgice tun rasuwar nan shi karan kanshi junior  bakya bashi kulawar da ta dace idan ke kika Gaza su kuma fa?"

Idanunta da suke a sussuntume tun rasuwar ta ɗaga ta kalli ummi tace cikin wani irin murya
"haka ne! Na gode ummi yanzu ina ga lokaci yayi da zan yi abunda ya dace, ba zan yi faɗa da YUSUF yanzu ba amma ba shi yake nufin ya sha a banza ba, yanzu ne na fara koyo daga karatun da duniya take koyar dani, zan yi bita in hardace a duk sadda na tashi amsa jarabawar baze yiwa kowa daaɗi ba saboda da 100/100 zan fita, yanzu zan iya yin duk abunda ya dace saboda yarana biyun nan da kuma fansar jinin Usman... YUSUF! hmmm"

Dukda ummi bata fahimci maganan ta ba, ita dae tunda tayi magana yau da sauki, abinci wadda ummi na shigowa gidan hidayat ta mika mata envelope da Moh Raed ya ajiye mata Dukda bata san waye shi ba ya taimaka mata har aka gama gaisuwar usman ba'a rasa abinci da ruwa ba.

A gabanta ta ajiye Seda ta kalli abincin na seconds kan mutumin ya faɗo mata a rai, Allah kaɗai ya san daga ina yake ya tsaya ya taimakesu ba tare da neman komai a wurinsu ba, ko ma dae menene she's so much indebted to him.

A ranan ummi ta koma gidansu ganin Hidayat ta dena koke koken ta natsu, kan Ummi ta tafi babu abunda bata mata ba har abinci ta sake girka wani ta sa a food flask ta ajiye mata, yamma Lis tana yiwa Junior wanka Aisha da yanzu babu yawan maganan tan nan na zaune gefe tayi tagumi kaman wata babba.

Kaman an jefo shi haka ya faɗo gidan tun daga dukan da yayi musu ita da Usman bata sake ganinshi ba se a yau Usman na kwana na bakwai zuwa takwas a rami, yadda ya shigo yasa Aisha firgita ta tashi da gudu taje ta faɗa jikin hidayat tana kankameta kaman zata shide take cewa

"Abba! Abba kayi hakuri don Allah karka dakemu... Ya Usman ya mutu nima karka kasheni karka rabani da mamana!"

Hawaye ne ya sulmiyowa hidayat ta ɗago rinannun idanunta ta zube a fuskanshi, haɗe rai yayi kaman wani mala'ikan ɗaukan rai yace
"ke ya ma sunanki? Wallahi kika kuskura na rike ki se na lahira ya fi ki jin daaɗi"

Hidayat bata sake Kallonshi ba ta ɗago ta tana share mata hawayen dake zuba tace
"karki sake kuka Aishana ai yanzu kuma me dukanki se ruwan sama shi ɗin ma se in na bari, ki dena kukan nan bana so"

Har ya wuce ya dawo yace
"me kike cewa?"

Mikewa tayi tare da ajiyewa Aisha junior a cinyar ta ta kalleshi cikin idanu tace
"nace me taɓa ta kai har ma ni a yanzu kam se ruwan sama!"

"kina nufin ban isa taɓaku be kenan?"
Da mamaki yake maganan ganin ko ɗar babu a fuskanta se wani irin shakkar ta ya rufe shi da a da ne ze iya kai mata hannu zuwa yanzu.

"Yadda kunnuwanka suka ji"

"Ah lallai kan mage ya waye, karki manta a gidana kike kuma har yanzu ni mijinki ne, ita kuma wannan ƴata ce don haka ina da ikon yin yadda na ga dama a lokacin da na ga dama.."

KOWA YA GA ZABUWA...Where stories live. Discover now