Wacece Ni?
Story written by
DielaIbrahim ✍️Part 1/16
___________________________________
AbujaKamar kullin yauma na gama Duk aikin Daya Dace.......Nayi ma
Hayatee sai da safe kasancewar
Karfe goma lokacin
Don ita har tayi Shirin kwanciya
Na rufo Mata kofa
Taku biyu na qara Domin xuwa dakinmuAmma sai ji nayi an damki hannuna an janyo ni zuwa wani corridor din hade da toshe min bakida hannu
Dukda dare yayi, An kashe wutar corridor din
Amma Ina iya gani fuskanshi saboda hasken farin wata Daya haska wajan daga tsakiyar corridor din wajan a bude yake
Shi Kuma Yana kokarin fadin
Shhishhhhii 🤫
Alamar karnayi ihuTsayawa yayi sannan yace ki nutsu magana kawai xamuyi
Sosai abin yaban mamaki
Meke Shirin faruwa Kuma Dani
Ina cikin zaman zamana
Hankali na kwance......Katse min tunani yayi da cewa
Miye sunankiBanyi niyan tanka mashi ba
Amma ahankali na furta
BODDOwow wat a nice name
Amma dai ke ba Yar aiki bace
Don dagani bakiyi Kama da masu aiki baNidai tsoron sa nakeji
Jikina na kyarma muryata na rawa da kyar na samu nace dashi
Bawan Allah me kake nema nee
awaje naShhishhhhii 🤫 ya qara cewa nai Shuru
Cen Kuma yace kawai kin burge nine Ina Jin kaman San ki nakeKije kiyi tunani Kinji ko young lady kiyi tunani ko xaki iya aure na gobe xamu hadu sai mu qarasa
Toh nace mashi da sauri don ni gaskiaya na qosa na bar wajan kada wani ya ganni
Da gudu na koma daki
Ina haki
Mama ta lura da hakan tace
Boddo yarinya ta me ya sameki ne?Amma saina tsinci kaina da boye Mata saboda bansan me xatayi tunani akan hakan ba
Ohhh Allah you keep on testing me all the time
Allah ka bani ikon cin jarabawar ka kodame taxo minAfili Kuma nace Mama
Babu komai naji tsoro nee saboda nikadai nee a corridor din gashi dare yayiMama Tai dariya kadan tace
Ki rage tsoro Boddo
Yooo me xai ciki a corridor din
Babu fa Wanda xai shigoNi Zo ki zauna In qara samaki labarinki kin ishe ni kullin
Da na karasa makiNikam jinayi bani son Jin wani labari yanxu saboda a zahiri gaskia tsoro nakeji wannan mutumin me yake nufi
Kaman akwai personal abinda ya kawo shi ba soyayyar asali bane
Amma dasannu xan bishi ahankali inshallah Allah baxai bashi ikon cutar Dani ba
Saurin kawar da xancen nayi kada mama ta gane abinda ke zuciyataGuri na samu kusa da Mama nace Mama na kosa naji
Afara pleaseHmm Mama tayi murmushi
Tace kamar yadda nake fada maki Boddo
Alhji. Mata biyu yake dashi
Babbar matar sa tana zaune a wani gari nee daban it da danta
Wannan flat din da kika gani a kulle to natane
Danta Daya Kuma shine Babba agidan gaba daya
Kafin shi ta haihu har sau biyu du Maza Amma Allah Bai bar Mata ba sai ana uku nee Allah SWT yabar mata Wanda haryanxu karatu yakeyi Bai gama baSai matar sa ta biyu itace mummy qarama
Ita yaranta biyu
Abuldarr da Kuma LailaDuk fadin gidan Nan iyakan yaran da Allah yabawa Alhaji kenan
Kuma ko wani mutun Yana da flat dinsa kamaryadda kika gani
Gobe in Allah ya kaimu xan xagaya dake gidan gaba daya don na nuna maki komai sai dai xamu gaji fah saboda gidan ba kadan ba wajan girmaMurmushi nayi nace Mata ba komai Mama
Nikam ma na Saba da aiki baxan gaji ba inshallah
Mama ke ma Baki da Yara nee
Ina zuri'ar ki?
Mama Tai murmushi tace
Boddo yarinya ta guda Mai kimanin shekara Ashirin da dori kadan ya rage ta Shiga Talatin
Ita kadai Allah ya mallaka min
Tai Shuru for a whileMama ya kikayi Shuru Kuma
Ko ta mutu ne and Ina mahaifin taBoddo kenan kina da son Jin labari....mahaifin yata Allah yai Masa Rasuwa shekaru Ashirin kenan, diyata Mai suna Halima Kuma tana gidan mijin ta ayanxu Haka tana da 'ya'ya Hudu jikokina kenan
Sukanxo ai xaki gansu wata tanaToh Mama Allah ya kaimu lakacin da xasu xo
Ameen
Mama tayi murmushi kin gaji da yawa xo ki kwanta ki huta koToh Mama na fada Ina Hamma
Na kwanta kenan na fara tunanin halin da Baba yake ciki
Allah sarki baba ko yayi Daya dawo ya tadda bananan
Allah ya qara Masa lafiya
Ya Kuma bani ikon daukan dawainiyan shi nan gaba
Na Dade Ina tunanin Baba har bacci mai nayi yai awan gaba Dani...........
Washegari
10am
Nagama abinda nakeyi
Na fita daga cikin dakin Hajiya don batanan tana wajan Alhaji
Na fita don na wanke mopper da towel a waje saboda bana Jin dadin wankewa a bayi, ba jimawa na gama na dan zagaya tabaya kadan inda nake shanyawa wajan wasu fulawoyi na gama shanyawa
Na juya kenan xan wuce
Naga mutun agabanaGira ya daga min
Hade da min turanci
How far?Saukar da kaina nayi kasa na gitta ahankali xan wuce
Amma Kuma Kash hannuna yaso kamawa ya sabule yaji ya rike hijabKallona yayi cikin mamaki
Sai ya wayence kamar babu komai yace kada Kiyi gigin Fadi ma wani wannan maganar
Tsakanin mu ne
It's a secret
Har ya tafi Sai Kuma ya dawo
Na manta ku masu aiki Baku fiye Jin turanci ba
Ina nufin wannan maganar sirri nee tsakanina dake
Sannan ya wuceSosai hankali na ya tashi narasa Ina xansa kaina sabon Al'amari na Shirin faruwa Dani
..............,....
DielaIbrahim ✍️
Vote/Share please
YOU ARE READING
WACECE NI ✔
Non-FictionAlmost true life story.. it's deals with challenges,with so much difficulty in life...