Wacece Ni?
Part 2/3
______________________Next Day
In the morning 10:30Ina daki Ina ta faman aiki
Bayan na gama na part din Hayatee, na karasa gyara part dinmu..............Ina zaune saman gado naji nidai hankalina Bai kwanta da mafarkin danayi ba
Don Haka na janyo waya ta na Kira Goggo a karo na biyu
Nayi sa'a kuwa ta dauka sai dai naji muryan DijeNace Dije kina gidan Goggo ne
Tace Eh
Nace ya goggo take
Tace tana lafiya
Nace Baba fah Yana Nan kuwa Ina so nayi magana dashi?Tace toh Baba bayanan
Nace toh don Allah idan ya dawo ko ma yaushe nee ku kirani can Kira ku kinji........tace toh
Na kashe wayar Ina mita Duk Baba nee ya Hana na siya mashi waya da yanxu ban Kira shi ba..............
Yauma kaman kullin haka naki xuwa wajan Ummie
Idan Mama ta shigo Kuma nakan tambayeta Hayatee sai tace ai jikanta na tare da ita
Ni Kuma sai nayi xama na a daki kawai..,..............________________________________________
Tsahon kwana biyu nayii bana fita ko dakin Hayatee bana xuwa
Abinda yafi damuna shine mafarkai akan Baba danakeyi
Sosai tsahon kwana biyunnan
Koda da Rana nee sai nayi mararkinshi... Nidai abin ya ishe Ni don Haka na Yankee shawaran xuwa na nemi izinin Hayatee ko xata barni naje Naga BabaNa fita xuwa dakinta Amma ban sameta ba..... .nai wani tunani dabara ta fado min na fita waje don na shakata kafin Hayatee ta dawo
Ina zaune a Babban garden din gidan.....wajan yayi sanyi saboda yawan bishiyoyin dake wajan ga ruwa adan karamin wani waje Mai kaman rafi sannan ta want bangare Kuma anyi wani round about ruwa nee keta yawo awajan daga wannan karamin rafin ya tafi xuwa roundabout din Wanda ta Bayan wajan tiles nee kewaye sannan aka jera kujeru Kuma akayi runfa............Bakajin komai sai sautin tsuntsaye da Kuma ruwa
Lallai garden din abin birgewa nee saboda kyan da yake dashi
Masha Allah na fada a RainaNikam Ina zaune akasan wani green grass nayi tagumi
Hayaniya na fara ji ta bayana
Muryoyin su Hayatee neBan waiga ba har suka iso garden din ita da Ummie nee dabn Kuma Adda.........suna hira suna raha abin gwanin ban sha'awa
Lahhhh kunga Yar halak
Hayatee ta fada
Ummie tace Boddo Wai laifi mukayi nee aka sharemu kwana biyu ta fada tana dafaniNayi murmushi nace Ina aa Ummie.....Na bar Hayatee nee ta tarbi jikanta dakyau.....Nima bana Jin dadi nee ko mama ban Fadi mawa ba
Meyasa meki Boddo Adda ke tambaya
Na juya na kalli Adda nace
Mura nakeyi Aunty Amma naji saukiTo Allah ya kara sauqi....mu karasa cen mu zauna ko....yauwa Boddo je flat dina ta dinning xaki ga kayan marmari an shirya ki dauko pls cewar Ummie
Na amsa da toh na wuce Ina mamakin yanda Hayatee take da yayanta kwata kwata baxaka dauka cewa yayanta bane
Itakam Mummy Bata Shiga sabgar su......Suma dai Basu Shiga sabgarta nikam xaman nasu na ban mamaki.......alokacin
Na Shiga kaitsaye dinning na nufa Amma ta corridor Ina cikin tafiya zuwa dinning din naji na bige mutum wanda kaina yai masauki a faffadan kirjin sa, kanshin turarensa Mai dadi shi ya daki hanci na......idanuwa na a lumshe suke Ina tsoron kada na bude Naga Abuldarr saboda A'yan kwanakinnan Ina yawan haduwa dashi...............daurewa nayi na bude idanu, babu abinda nayi tozali da wani kyakkyawan azurfa a yatsanshi na tsakiya
Da bisani Kuma xan dauke kaina kenan na hango kyallin wani zoben azurfa nakara Kai duba na dakyau wanda yai min kama da zobena tun Ina karaama Baba ya tsiya min da tsadanshi.........,daga kaina nayi nadan ja da baya Ina mamakin ganin zoben a akaramin yatsanshi........sai nai saurin daga idanuwa na na kalle shi..................
I've seen him somewhere before
Ovcux his face look familiar to me .........but I can't recall anything
YOU ARE READING
WACECE NI ✔
Non-FictionAlmost true life story.. it's deals with challenges,with so much difficulty in life...