Page....15.....

171 21 0
                                    

      
    🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵🏵
    ..............*KAICO NAH*.............
Rubutawa.......sadi-sakhna.......


DEDICATED TO MY MOTHER & UNKNOWN OLD WRITER

Wattpad:SAKHNA03

🏵🏵🏵
...15....

Sanyin asuba ne ya busa sumayya,wanda hakanne ya zamo sanadiyyar farfadowarta daga suman da tayi a dukan da mutari yayi mata.
Yunkurawa tayi zata tashi amma ciwo yace gashinan zuwa,dan wani bala'in ciwone ya ziyarci mararta,kara ta saki cikin mawuyacin hali kafin ta daure ciwon ta mike tsaye,dan tasan babu wanda zai kawo mata agaj koda kuwa numfashintane yake shirin fita na karshe kaman yanda taga kallon da suke mata jiya.
Dakinnasu ta shiga tana daddafa bango har ta kai bakin gadon ta zauna.
Waiga fuskarta tayi ta kalli mutari ya baje sai bacci yake abinsa,wani bakim cikine ya kamata da ta tuna irirn dukan dayake mata tareda tsinewa iyayenta ta uwa ta uba,dan kawai ya ga wani a dakinsu,in kuwa zai mata shaida ai yasan ta kawo masa budurcinta,meyasa ma ta kasa ganin shi wane irin mutun ne har saida lokacin ya kure,tirr kuwa da irin wannan soyayya mai makance idanun mutum,kaico da irin taurin kai nata.
Gashi ta auri mijin daya zubar mata da ciki,mijin daya boyemata komai nasa,mijin da yakasa yarda da ita,mijin daya yi mata dukan da ko zata mutu bai damu ba,mijinda zai iya barinta a waje ta kwana a sume bai damuba.
Share hawayenta tayi tareda dawowa daga tunanin da ta tafi,karar kiran sallahr asuba ne ya sakata yunkurawa ta sake tashi ta nufi bandaki dan yin alwala.
Sallayarta ta shimfida tareda saka hijabinta ta tada sallahr nafila kafin a shiga sallah.
Dan ma Allah ya taimaketa tayi karatun addini dadai gwargwado.
Bayan tayi sallah addu'a take tayi wata ma bata san mai take fada ba saboda cika ha'ula'i da ta shiga.
"Aikin banza sai ayi ta sallah ana mika kai,nan kuwa mutum mazinacine mai cin amanar mijinsa"
Sallama sumayyah tayi tareda cewa,
"Duk abinda kake mutari ka cigaba dayi idan aiki alkhairi kakeyi,ka yanke min hukunci akan abinda kai kanka kasan ba gaskiya bane"
Magana take masa tana kuka amma ko a jikinsa sai ma tsuka da yayi tareda zuyawa yaci gaba da baccinsa.
Tana zaune akan sallayar har gari ya waye inna ta fito dora wutar kokonta,tashi tayi ta nade abin salahr tareda fita wajen,har sannan mutari bacci yake baiyi sallah ba.
Saurin dakatar da ita inna tayi tareda cewa,
"Kinga tsaya karki tabamin kayan sana'a kisaka min najasar zina,wato kin maidamu yan iska saiki kawo mana gardi gida kuna shekewa,kin iya kuma fallasa wata dan tayi,ai gwanda itama batada aure,kefah kinada aure kina cin amanar mijinkkin,nasan cikin jikinsa ma ba nasa bane,an kunso za'a kawomana muyi raino,tun wuri ki nemi uban cikin danki ehe"
"Haba inna karki fadi haka mana,yanzu abin har ya kai ki sheganta jikanki?"
"Kull ina rabaki karki kara danganta jinina da cikin dake jikinki,dan wallahi har abada bazan amsheshi ba,anyi walkiya munga komai ai"
Ita dai sumayya bata sake cewa komai ba sai komawa dakinsu da tayi,da alama zuwa yanzu abin yafi karfinta.
Shema'u da take bayan labule tana jin duk abinda ake,wata shewa tayi tareda kunna wayar ta kira wani,
"Hhhhh ai stone ina fada maka komai ya tafi yanda muka tsara,duk sun dauka cewar dagaske kai kwartonta ne,Baka ga yanda mutari yayi mata duka ba jiya da daddare,dadi kaman zai kasheni,hmmm ai naso ma ta kasa tashi yau ba ita munafuka ba.
Kuma ka birgeni da kace kayi masa shima duka jiyan,dama nasan zaka rama min ai,yanzu dai sai mun sake haduwa kawai"
Lokaci yadan ja har yakai zuwa yanzu cikin sumayyah yayi wata takwas yana shirin shiga wata na tara,wahala ta gidan duniya babu wanda bata sha ba kokuma take kan sha.
Ga karancin abinci mai gina jiki ga kuma aiki,sannan uwa uba ciwon mara wanda take fama dashi.
Fitowa tayi daga bandaki ta ajiye butar hannunta wacce ta wanke kafarta da kuma hannayenta.
Dakin nasu ta shige a kanjale kaman ba sumayyah ta da ba,dan duk wanda yaganta a yanzu ba lallai ya gane ta ba,ta rame babu komai a jikinta sai ciki kawai.
Mai ta dauko ta shafa kafin ta dauko yar atampa a cikin kayanta wacce ta adana,dan ma allah ya taimaketa kayanta basu gama karewa ba.
Wata koriyar atampa ta dauka ta saka tareda wani hijabi shima mai adon koren.
Bankada katifarsu tayi ta dauko wata gudar dari biyar a cikin wasu kudi da ta gani a wajen,daga yanda take daukan kudin kasan ba nata bane bata da gaskiya.
Ficewa tayi a gidan sikaf sikaf babu wanda ya ganta a cikin su inna da shema'u.
Tafiya take tana waige waige har tq iso bakin titi,dayake wajen da yar tazara har ta galabaita ta fita a hayyacinta sosai.
Wani mai acaba ta tara tareda yi masa kwantancen wani asibiti tace ya kaita .
Ajiyar zuciya tayi da taga an fara tafiya babu wanda ta hadu dashi da ta sanshi,kalle kalle take tayi a bakin hanyar,dan rabonta da fitowa daga cikin gidannasu wanda tayiwa lakabi da kurkuku tun ranar da ta shiga ciki.

KAICO NAHWhere stories live. Discover now